Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya
Published: May 11, 2026 at 5:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Najeriya Da Maroko Za Su Kulla Yarjejeniya a fannin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayya

Alaƙar diplomasiyya tsakanin kasashen Najeriya da Maroko ta kara nuna ƙarfafa, inda kasashen biyu suka kulla yarjejeniyar karfafa dangantaka a fannonin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayya.

Wannan sanarwa ta fito ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin Ministar Harkokin Wajen Najeriya, Bianca Ojukwu, da takwaranta na kasar Maroko, Nasser Bourita.

Babban kashin bayan tattaunawar shi ne aikin ginin bututun iskar gas na Najeriya da Maroko (African Atlantic Gas Pipeline). Ministocin biyu sun bayyana wannan gagarumin aiki a matsayin “mai canza alkiblar tattalin arziki” wanda zai samar da tsaro a fannin makamashi da kuma dunkulewar yankin Afirka ta Yamma baki daya.

Ma’aikatar Harkokin Wajen ta tabbatar da cewa tuni kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) da takwaransa na kasar Maroko (ONHYM) suka kammala binciken fasaha na aikin. Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Sarki Mohammed VI za su sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin a rubuce kafin karshen rubu’i na hudu na wannan shekara.

Baya ga batun iskar gas, kasashen biyu sun tattauna hanyoyin hadin gwiwa wajen sarrafawa da rarraba takin zamani. Wannan mataki na da nufin tabbatar da wadatar abinci ba kawai a kasashen biyu ba, har ma da sauran sassan nahiyar Afirka.

Domin farfado da tsoffin yarjejeniyoyin da aka kulla tun zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2018, Najeriya na shirin karbar bakuncin taron hadin gwiwa na kasashen biyu (Bilateral Joint Commission) karo na biyu.

Haka zalika, ministocin sun jaddada bukatar sake kafa Majalisar Kasuwanci ta Najeriya da Maroko. Sun bayyana cewa yarjejeniyar cinikayya ta bai-daya ta nahiyar Afirka (AfCFTA) da kuma shirin kauce wa biyan haraji ninki biyu, za su bude sabbin kofofin bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja
Next Post: Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita Labarai
  • Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
  • Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi Afrika
  • Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.