Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP
Published: December 7, 2025 at 10:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 7, 2025

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar, ya yi jawabi ga sojojin rundunar Birget na 25 na Sojin Najeriya, inda ya bayyana goyon bayan jihar ga yakin da suke yi da ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP.

Gwamnan, wanda ke jawabi a sansanin sojoji a Damboa, ya tausaya wa jami’an da sojoji, yana mai godiya ga dimbin sadaukarwar da suka yi da kuma kokarin da suke yi a kullum.

Ya yaba wa abin da ya bayyana a matsayin “Namijin kokarinsu da kuma sadaukarwar su” a yakin da ake yi don kare Jihar Borno da kuma kare fararen hula daga barazanar Boko Haram da kuma Islamic State West Africa Province (ISWAP).

Zulum ya ce, “A madadin gwamnati da mutanen jihar Borno, Mun zo Damboa don yi muku jaje kan koma bayan da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin abokan aikin ku.

Yace Wannan lamari ne mai ban takaici, kuma ina so in mika ta’aziyyata gare ku da iyalan dukkan jami’ai da ma’aikatan wannan runduna da suka rasa rayukansu yayin da suke gudanar da ayyukansu tare da addu’ar Allah yabawa wadanda suka ji rauni a fagen daga lafiya da wuri-wuri.

Ga wadanda daga cikinku wadanda har yanzu suna raye kuma suna cikin koshin lafiya, muna addu’ar Allah ya kare ku, ya ba ku hangen nesa da karfin aiwatar da ayyukanku yadda ya kamata, sannan muna yabawa da goyon bayan ku kuma muna so mu yaba muku.

Gwamnan ya samu tarba daga Kwamandan Rundunar Sojoji ta 25, Brigadier Janar Igwe Patrick Omokeh.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na rangadin Zulum ga al’ummomi a kudancin Borno.

A farkon yinin ranar, gwamnan ya gana da iyalai dake cikin alhini a Chibok, inda ya yi musu ta’aziyya game da asarar rayuka da dukiyoyi, ya kuma yi ta’aziyya da kuma jaje ga waɗanda suka rasa kadarori.

A lokacin taron a Chibok, gwamnan ya sanar da matakai na musamman don kare rayuka da dukiyoyi. Ya lura cewa gwamnatin jihar, tare da haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, tana aiwatar da ƙarin matakai don kare al’ummomin da ke cikin mawuyacin hali daga hare-hare.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar
Next Post: Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ?

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
  • Chadi Ta Sauyawa ‘Yan Gudun Hijira Matsuguni Afrika
  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.