Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP
Published: December 7, 2025 at 10:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 7, 2025

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar, ya yi jawabi ga sojojin rundunar Birget na 25 na Sojin Najeriya, inda ya bayyana goyon bayan jihar ga yakin da suke yi da ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP.

Gwamnan, wanda ke jawabi a sansanin sojoji a Damboa, ya tausaya wa jami’an da sojoji, yana mai godiya ga dimbin sadaukarwar da suka yi da kuma kokarin da suke yi a kullum.

Ya yaba wa abin da ya bayyana a matsayin “Namijin kokarinsu da kuma sadaukarwar su” a yakin da ake yi don kare Jihar Borno da kuma kare fararen hula daga barazanar Boko Haram da kuma Islamic State West Africa Province (ISWAP).

Zulum ya ce, “A madadin gwamnati da mutanen jihar Borno, Mun zo Damboa don yi muku jaje kan koma bayan da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin abokan aikin ku.

Yace Wannan lamari ne mai ban takaici, kuma ina so in mika ta’aziyyata gare ku da iyalan dukkan jami’ai da ma’aikatan wannan runduna da suka rasa rayukansu yayin da suke gudanar da ayyukansu tare da addu’ar Allah yabawa wadanda suka ji rauni a fagen daga lafiya da wuri-wuri.

Ga wadanda daga cikinku wadanda har yanzu suna raye kuma suna cikin koshin lafiya, muna addu’ar Allah ya kare ku, ya ba ku hangen nesa da karfin aiwatar da ayyukanku yadda ya kamata, sannan muna yabawa da goyon bayan ku kuma muna so mu yaba muku.

Gwamnan ya samu tarba daga Kwamandan Rundunar Sojoji ta 25, Brigadier Janar Igwe Patrick Omokeh.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na rangadin Zulum ga al’ummomi a kudancin Borno.

A farkon yinin ranar, gwamnan ya gana da iyalai dake cikin alhini a Chibok, inda ya yi musu ta’aziyya game da asarar rayuka da dukiyoyi, ya kuma yi ta’aziyya da kuma jaje ga waɗanda suka rasa kadarori.

A lokacin taron a Chibok, gwamnan ya sanar da matakai na musamman don kare rayuka da dukiyoyi. Ya lura cewa gwamnatin jihar, tare da haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, tana aiwatar da ƙarin matakai don kare al’ummomin da ke cikin mawuyacin hali daga hare-hare.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar
Next Post: Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ?

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
  • Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.