Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP
Published: December 7, 2025 at 10:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 7, 2025

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar, ya yi jawabi ga sojojin rundunar Birget na 25 na Sojin Najeriya, inda ya bayyana goyon bayan jihar ga yakin da suke yi da ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP.

Gwamnan, wanda ke jawabi a sansanin sojoji a Damboa, ya tausaya wa jami’an da sojoji, yana mai godiya ga dimbin sadaukarwar da suka yi da kuma kokarin da suke yi a kullum.

Ya yaba wa abin da ya bayyana a matsayin “Namijin kokarinsu da kuma sadaukarwar su” a yakin da ake yi don kare Jihar Borno da kuma kare fararen hula daga barazanar Boko Haram da kuma Islamic State West Africa Province (ISWAP).

Zulum ya ce, “A madadin gwamnati da mutanen jihar Borno, Mun zo Damboa don yi muku jaje kan koma bayan da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin abokan aikin ku.

Yace Wannan lamari ne mai ban takaici, kuma ina so in mika ta’aziyyata gare ku da iyalan dukkan jami’ai da ma’aikatan wannan runduna da suka rasa rayukansu yayin da suke gudanar da ayyukansu tare da addu’ar Allah yabawa wadanda suka ji rauni a fagen daga lafiya da wuri-wuri.

Ga wadanda daga cikinku wadanda har yanzu suna raye kuma suna cikin koshin lafiya, muna addu’ar Allah ya kare ku, ya ba ku hangen nesa da karfin aiwatar da ayyukanku yadda ya kamata, sannan muna yabawa da goyon bayan ku kuma muna so mu yaba muku.

Gwamnan ya samu tarba daga Kwamandan Rundunar Sojoji ta 25, Brigadier Janar Igwe Patrick Omokeh.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na rangadin Zulum ga al’ummomi a kudancin Borno.

A farkon yinin ranar, gwamnan ya gana da iyalai dake cikin alhini a Chibok, inda ya yi musu ta’aziyya game da asarar rayuka da dukiyoyi, ya kuma yi ta’aziyya da kuma jaje ga waɗanda suka rasa kadarori.

A lokacin taron a Chibok, gwamnan ya sanar da matakai na musamman don kare rayuka da dukiyoyi. Ya lura cewa gwamnatin jihar, tare da haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, tana aiwatar da ƙarin matakai don kare al’ummomin da ke cikin mawuyacin hali daga hare-hare.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar
Next Post: Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ?

Karin Labarai Masu Alaka

An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai
Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
  • Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
  • Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
  • Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.