Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa
Published: December 8, 2025 at 10:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 8, 2025

Gwamnatin jihar Adamawa ta ayyana dokar hana fita na sa’o’i 24 a karamar hukumar Lamurde, sakamakon sake barkewar rikici a yankin.

Wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan jihar Hussaini Hammangabdo, ya fitar a ranar Lahadi ta bayyana cewa an dauki matakin ne bayan sake tashin wata takaddama tsakanin al’ummomin yankin da yammacin ranar Lahadi.

A makon da ya gabata, al’ummomin Bachama da Chobo na karamar hukumar Lamurde sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a dakin taro na Banquet Hall da ke fadar Gwamnati a Yola.

Taron ya hadu da Hama Bachama, Homun Daniel Ismaila, manyan jiga igan al’umma, jami’an gwamnati da hukumomin tsaro.

Sanarwar ta kara da cewa: “Tuni an umurci hukumomin tsaro da su dauki matakan gaggawa domin dawo da zaman lafiya da doka a yankin.”

Gwamnati ta kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da nuna da hadin kai domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s
Next Post: Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma

Karin Labarai Masu Alaka

Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba Amurka
Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika
Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana Afrika
Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
  • Kasar Masar Ta Dakatar Da Wasu Ayyukan Da Ake Amfani Da Man Fetur Da Diesel Labarai
  • Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
  • Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki Amurka
  • Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.