Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su
Published: January 1, 2026 at 10:44 AM | By: Bala Hassan

Kasashen Mali da Burkina Faso sunce za su hana Amurkawa izinin shiga kasashen su, martani kan irin wannnan matakai da gwamnatin Trump ta bada sanarwa akai a farkon watan Disemban 2025.

A cikin sanarwar da ma’aikatun harkokin kasashen wajen biyu suka bayar daban-daban a daren  litinin, kasashen biyu da suke Afirka ta yamma sunce suna daukar wannan matakine a zaman “martani” bayanda fadar White House ta bada sanarwar ranar 16 ga watan disemba cewa shugaban Amurka Donald Trump, zai kara kasashen su da wasu biyar a jerin kasashen da Amurka zata iya haramtawa shiga kasar.

Fadar White House tace jerin kasashen da matakin zai shafa zai fara aiki daga  1 ga watan Janairu na sabuwar shekara, ya shafi kasashe da suka ci gaba nuna rashin tantan-cewa na kwarai, yin kididdiga, da kuma musayar bayanai domin kare Amurka ta fuskar tsaro da kuma barazana kan zaman lafiya.

Mali ta fada a talata cewa shawarar da hukumomi a Washington suka dauka na sanya kasar cikin jerin kasashen da zata haramtawa shiga, ta yi hakan ne ba taredaa wata tuntuba ba, kuma hujjar data bayar na yin haka yayi karo da hakikanin al’amura.

Kasashen Mali da Burkina Faso ba sune kasashe na farko da suka dauki irin wannan mataki da ya shafi Amurkawa ba, bayan gwamnatin Trump ta auna su da irin wannan mataki.

Ranar 25 ga watan  Disemba da ta wuce kasar Nijar makwabciyar wadannan kasashe ta bada sanarwar cewa zata daina bada Visa ga Amurkawa, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka fada, daga bakin masana harkokin difilomasiyyar kasar.

A cikin watan Yuni ne kasar Chadi ta bada sanarwar dakatar da bada visa ga Amurkawa, bayan da gwamnatin Amurkan ta saka kasar a jerin kasashe 12 da haramcinta shafa.

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro.
Next Post: Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai

Karin Labarai Masu Alaka

Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika
Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.