Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su
Published: January 1, 2026 at 10:44 AM | By: Bala Hassan

Kasashen Mali da Burkina Faso sunce za su hana Amurkawa izinin shiga kasashen su, martani kan irin wannnan matakai da gwamnatin Trump ta bada sanarwa akai a farkon watan Disemban 2025.

A cikin sanarwar da ma’aikatun harkokin kasashen wajen biyu suka bayar daban-daban a daren  litinin, kasashen biyu da suke Afirka ta yamma sunce suna daukar wannan matakine a zaman “martani” bayanda fadar White House ta bada sanarwar ranar 16 ga watan disemba cewa shugaban Amurka Donald Trump, zai kara kasashen su da wasu biyar a jerin kasashen da Amurka zata iya haramtawa shiga kasar.

Fadar White House tace jerin kasashen da matakin zai shafa zai fara aiki daga  1 ga watan Janairu na sabuwar shekara, ya shafi kasashe da suka ci gaba nuna rashin tantan-cewa na kwarai, yin kididdiga, da kuma musayar bayanai domin kare Amurka ta fuskar tsaro da kuma barazana kan zaman lafiya.

Mali ta fada a talata cewa shawarar da hukumomi a Washington suka dauka na sanya kasar cikin jerin kasashen da zata haramtawa shiga, ta yi hakan ne ba taredaa wata tuntuba ba, kuma hujjar data bayar na yin haka yayi karo da hakikanin al’amura.

Kasashen Mali da Burkina Faso ba sune kasashe na farko da suka dauki irin wannan mataki da ya shafi Amurkawa ba, bayan gwamnatin Trump ta auna su da irin wannan mataki.

Ranar 25 ga watan  Disemba da ta wuce kasar Nijar makwabciyar wadannan kasashe ta bada sanarwar cewa zata daina bada Visa ga Amurkawa, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka fada, daga bakin masana harkokin difilomasiyyar kasar.

A cikin watan Yuni ne kasar Chadi ta bada sanarwar dakatar da bada visa ga Amurkawa, bayan da gwamnatin Amurkan ta saka kasar a jerin kasashe 12 da haramcinta shafa.

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro.
Next Post: Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai

Karin Labarai Masu Alaka

CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
  • Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
  • Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
  • Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran Afrika
  • Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.