Dakarun Operation Fansan Yamma sun ceto fararen hula 48 da aka yi garkuwa da su a jihar Zamfara bayan sun dakile wani hari da ‘yan ta’adda suka kai da sanyin safiyar Asabar a ƙauyen Magami da ke Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda.
A wata sanarwa da Mai Bayar da Bayanai na Rundunar Hadin Gwiwa ta Operation Fansan Yamma, Laftanar Kanar Aliyu Danja, ya fitar, ya ce dakarun Sector 2 sun samu kiran gaggawa cewa wasu ‘yan ta’adda kimanin mutum 40 da ke kan babura sun mamaye ƙauyen Magami.
Da isar dakarun wurin, sun fafata da ‘yan ta’addan a wani mummunan artabu. Sakamakon matsin lambar da sojojin suka yi musu, ‘yan ta’addan sun yi watsi da mutanen da suka sace tare da tserewa cikin daji.
Sanarwar ta ce farar hula guda ta rasa ranta yayin harin, yayin da wasu biyu suka samu raunukan harbin bindiga, kuma an garzaya da su zuwa Babban Asibitin Kaura Namoda domin samun kulawar likita.
Bayan kammala aikin ceton, dakarun sun ƙaddamar da sintiri mai ƙarfi a yankin Magami da dazukan da ke kewaye domin tabbatar da tsaro da hana sake kai hare-hare.
Rundunar ta yaba da jarumtaka da ƙwarewar dakarun wajen gudanar da wannan aiki cikin nasara, tare da sake jaddada aniyarta na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a yankin Arewa maso Yamma.


