Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe
Published: July 28, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Raya Yankin Kudancin Gombe (Gombe South LCDA), Auwal Jauro Bapp, tare da mataimakinsa, Dalhatu Boderi, sun yaba da shirin rabon kayan tsaftar al’ada ga ‘yan mata da Alhaji Jalo Wali ya ƙaddamar. Sun bayyana shirin a matsayin wani muhimmin mataki da ya zo kan lokaci domin inganta lafiyar mata da kuma ƙarfafa ‘ya’yan mata su ci gaba da karatunsu ba tare da tangarda ba.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban LCDA ya tabbatar wa masu shirya shirin da cikakken goyon baya da haɗin kai daga hukumarsa domin tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri.

A nata jawabin, Shugabar Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Jauro Tudun Wada (GJSS), Zulaihat Kabir, tare da Auwalu Mai Matasa Pantami, Mahmud Abubakar Wamban Pantami da Hajiya Maimuna Saleh Abdu, sun yi tsokaci kan nasarorin da gwamnatin Gombe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta samu a fannoni daban-daban.

Sun kuma yi kira ga masu hannu da shuni da ƙungiyoyi masu zaman kansu su haɗa hannu da gwamnati wajen tallafa wa mata da yara a faɗin jihar.

Tun da farko, wanda ya assasa shirin, Alhaji Jalo Wali, ya bayyana cewa haɗin gwiwar da suka yi da Alhaji Sa’adu Ali Mai Silifas na da burin raba fakiti ɗari na kayan tsaftar al’ada ga ‘yan mata a makarantun firamare da ke dukkan ƙananan hukumomi goma sha ɗaya na jihar Gombe.

Ya ce manufar shirin ita ce wayar da kan ‘yan mata kan tsaftar al’ada tare da samar musu da kayan da za su taimaka musu su ci gaba da karatunsu cikin walwala.

Alhaji Jalo Wali ya kuma bayyana Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar gwamna da ya cancanta, tare da yin kira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da yi wa dukkan ‘yan takarar Jam’iyyar APC addu’ar samun nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Gombe, Saleh Idris, da Sakataren Ilimi na ƙaramar hukumar wanda Abubakar Muhammad Bello (Bunun Gombe) ya wakilta, sun yaba wa Gombe Charity for Men and Women initiatives Foundation ƙarƙashin jagorancin Alhaji Jalo Wali da Alhaji Sa’adu Ali Mai Silifas bisa wannan shiri na jin ƙai.

Sun yi addu’ar Allah Ya saka musu da alheri tare da ƙara musu ƙarfin gwiwar ci gaba da gudanar da ayyukan tallafawa mata da ‘ya’yan mata a jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Rumbun Hotuna, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Next Post: Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka
Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
  • AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci Labarai
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.