Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji
Published: July 28, 2026 at 4:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitin Aiwatar da Fararen Takardar Kula da Filayen Kiwo a Jihar Gombe, ƙarƙashin jagorancin Dakta Ardo Chindo Abubakar, ya kai ziyarar aiki zuwa Masarautun Billiri da Pindiga domin ci gaba da wayar da kan al’umma da kuma tabbatar da aiwatar da manufofin gwamnati na samar da zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma.

A lokacin ziyarar a Billiri, Shugabar Ƙaramar Hukumar Billiri, Hajiya Eglah Idris, ta tarbi mambobin kwamitin tare da tabbatar musu da cikakken goyon baya da haɗin kai wajen sauke nauyin da aka ɗora musu.

Ta roƙi kwamitin da ya yi la’akari da bai wa manoman da suka riga suka noma a cikin filayen kiwo damar girbe amfanin gonakinsu na bana kafin a fara cikakken aiwatar da dokokin, bisa amincewar hakimai da shugabannin ƙauyuka.

Da yake mayar da martani, Shugaban Kwamitin, Dakta Ardo Chindo Abubakar, tare da Daraktan Gandun Daji na Jihar Gombe, Alhaji Musa Suleiman Kumo, sun bayyana cewa wannan shawara abin maraba ne, tare da alƙawarin yin nazari a kanta yayin aiwatar da matakan gwamnati.

Dakta Ardo Chindo ya bayyana cewa kwamitin ya fuskanci ƙalubale a wasu sassan jihar sakamakon rikice-rikicen da ke faruwa tsakanin makiyaya da manoma, amma ya jaddada aniyarsa ta ƙara ƙaimi wajen tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

A Masarautar Pindiga kuwa, Hakimin Garin Galadima, Alhaji Muhammad Kawuwa Ahmad, ya ce a wasu lokuta hukumomin gargajiya ba sa samun bayanan wasu matsaloli tun da wuri, lamarin da ke haddasa ta’azzarar rikice-rikice.

Hakimin ya buƙaci al’umma su ci gaba da zaman lafiya da juna tare da mara wa manufofi da shirye-shiryen gwamnati baya domin samun ci gaba.

Shi ma Shugaban Hukumar Raya Karkara ta Pindiga (LCDA), Alhaji Garba Yakubu, Walin Pindiga, ya yaba wa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa samar da yanayi na zaman lafiya da inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ya kuma tabbatar wa kwamitin da cikakken goyon baya wajen aiwatar da shawarwarin Farar Takarda domin samar da mafita mai ɗorewa ga rikice-rikicen makiyaya da manoma.

A nasa jawabin, Hakimin Kolmani, Barrista Muhammad Magaji Ibrahim, ya buƙaci a ɗauki tsauraran matakai kan duk masu mamaye filayen kiwo da gandun daji ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce duk wanda aka samu da laifin sayar da filayen kiwo ko hanyoyin shanun gwamnati ya kamata a hukunta shi bisa tanadin doka domin hana sake aukuwar irin wannan matsala.

Har ila yau, Daraktan Gandun Daji, Alhaji Musa Suleiman Kumo, ya yi kira ga masu sare bishiyoyi ba tare da izini ba da su daina wannan danyen aiki, yana mai buƙatar al’ummar jihar su kasance masu bin doka tare da bai wa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya cikakken haɗin kai wajen tabbatar da ci gaba mai ɗorewa da zaman lafiya a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe
Next Post: Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
  • Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika
  • Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.