Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta jihar Gombe (GOSERC) ta gudanar da wani muhimmin taro da mahukuntan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Savannah, a wani mataki na ƙarfafa haɗin gwiwa domin inganta rabon wutar lantarki a faɗin Jihar Gombe.
Da yake zantawa da Manema labarai bayan kammala taron, Shugaban Hukumar, Dakta Usman Abba Arabi, ya bayyana cewa manufar taron ita ce samar da dabarun haɗin gwiwa da za su tabbatar da inganta samar da wutar lantarki ga al’ummomin jihar.
Ya ce Gwamnatin jihar Gombe ce ta kafa Hukumar GOSERC domin tsara da kuma sa ido kan harkokin kasuwar wutar lantarki a yankunan karkara da birane, tare da tabbatar da cewa masu amfani da wutar lantarki sun samu ingantaccen sabis.
Dakta Usman Abba Arabi ya jaddada cewa Hukumar za ta ci gaba da aiwatar da ayyukanta yadda ya kamata, yana mai bayyana fatan cewa nan ba da jimawa ba al’ummar jihar za su fara cin gajiyar ingantacciyar, tabbatacciya kuma mai sauƙin samu ta fuskar farashi.
A nasa jawabin, Jagoran Tawagar Kamfanin Savannah Electricity Distribution Company, Abiddeen Olariwaju, ya bayyana cewa kamfanin sabon reshe ne na Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Jos (JED), wanda aka kafa bayan fara aiki da Dokar Wutar Lantarki ta shekarar 2023, wadda ta bai wa jihohi damar tsara da gudanar da kasuwar wutar lantarki a yankunansu.
Olariwaju ya ce kamfanin ya tanadi tsare-tsare na gajeren lokaci, matsakaicin lokaci da kuma na dogon lokaci domin bunƙasa samar da wutar lantarki a Jihar Gombe.
Ya ƙara da cewa an riga an fara gyaran na’urorin rarraba wutar lantarki (transformers) a garin Bajoga, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Funakaye, da kuma wasu sassa na cikin birnin Gombe, a matsayin matakin farko na aiwatar da shirin.
Ya tabbatar da cewa kamfanin zai ci gaba da aiki tare da Hukumar GOSERC da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da samar da ingantacciyar wutar lantarki ga daukacin al’ummar jihar Gombe.
Har ila yau, Olariwaju ya yaba wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa rattaba hannu kan Dokar Wutar Lantarki ta jihar Gombe, yana mai cewa hakan ya sanya Gombe cikin jihohi goma na farko a Najeriya da suka kafa cikakkiyar hukuma mai kula da harkokin wutar lantarki a matakin jiha.


