Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da rushe Kwamitin Shugaban Ƙasa mai kula da aiwatar da harkokin sayar da kaddarorin Gwamnatin Tarayya (Presidential Implementation Committee – PIC), tare da ba da umarnin aiwatar da matakin nan take.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, inda ya bayyana cewa daga yanzu dukkan harkokin da suka shafi ayyukan kwamitin za su koma ƙarƙashin kulawar Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Prince Lateef Fagbemi.
Sanarwar ta tuna cewa an kafa kwamitin ne a shekarar 2000, a zamanin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, domin kula da sayarwa da bayar da hayar filaye da sauran kaddarorin Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin tsarin Monetisation Policy.
Ta ce bayan nazari mai zurfi, Gwamnatin Tarayya ta gano cewa ayyukan kwamitin sun kauce daga ainihin manufar da aka kafa shi domin aiwatarwa, lamarin da ya janyo ƙararraki masu yawa a kotuna a sassan ƙasar nan.
A sakamakon haka, gwamnatin ta yanke hukuncin cewa babu wata buƙatar ci gaba da wanzuwar kwamitin.
Saboda haka, Shugaba Tinubu ya umarci a rushe kwamitin daga ranar 5 ga Nuwamban 2025, tare da ɗora wa Babban Lauyan Tarayya alhakin kula da dukkan harkokin da suka shafi ayyukan kwamitin.
Haka kuma, Shugaban Ƙasar ya umarci tsohon Sakataren kwamitin, B. S. Dutsin-Ma, da ya dakatar da duk wani aiki ko wakilci da yake yi a madadin kwamitin ko Gwamnatin Tarayya kan duk wani lamari da ya shafi ayyukansa.
Sanarwar ta ce matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na inganta yadda ake tafiyar da harkokin kadarorin gwamnati cikin tsari, gaskiya da inganci.


