Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa
Published: January 21, 2026 at 5:38 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomi a kasar Togo sun kame tare da korar tsohon shugaban kasar Burkina Faso, Paul Henri Damiba, zuwa kasar sa ta haihuwa, bayan da gwamnati ta zarge shi da laifin yunkurin juyin mulki, kamar yadda wasu majiyoyi 2 suka shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar Talata.

Paul Henri Damiba, ya karbi ragamar mulki ne a shekarar 2022, bayan da aka yiwa gwamnatin farar hula ta Burkina faso juyin mulki, wadda farin jinin ta ya dusashe saboda yawan tashin hankali da ake samu daga ‘yan ta’adda.

Rashin nasarar Damiba wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda, ya haifar da fushin sojin kasar, abinda ya jawo shima aka tsige shi a wannan shekarar, a wani juyin mulki karkashin Ibrahim Traore, wanda a yanzu shi ne shugaban kasar karkashin mulkin soja.

A farkon Wannan watan ne Burkina Faso ta sanar cewa ta dakile wani yunkuri na kashe shugaba Traore, da ake zargin Damiba ne ya shirya, wanda ya nemi mafaka a Lome, babban birnin kasar Togo.

Wani jami’in tsaro da wani dake da kusanci da shugaban kasar Togo sun shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters ranar Talata cewa An kama Damiba ranar Asabar, kuma An dauke shi a jirgi zuwa Ouagadougou, babban birnin Burkina Faso.

Togo ta tabbatar da fitar da Damiba daga kasar, inda ta ce ta yi haka ne, bisa bukata daga Burkina Faso.

Laifukan da ake tuhumar Damiba a Burkina Faso da su sun hada da almubazzaranci da wadaka da kudaden al’umma da halarta kudin haram, a cewar gwamnatin Togo

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama
Next Post: Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
  • Kasar Ghana Ta Tono Gold Na Miliyoyin Kudade Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.