Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa
Published: January 21, 2026 at 5:38 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomi a kasar Togo sun kame tare da korar tsohon shugaban kasar Burkina Faso, Paul Henri Damiba, zuwa kasar sa ta haihuwa, bayan da gwamnati ta zarge shi da laifin yunkurin juyin mulki, kamar yadda wasu majiyoyi 2 suka shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar Talata.

Paul Henri Damiba, ya karbi ragamar mulki ne a shekarar 2022, bayan da aka yiwa gwamnatin farar hula ta Burkina faso juyin mulki, wadda farin jinin ta ya dusashe saboda yawan tashin hankali da ake samu daga ‘yan ta’adda.

Rashin nasarar Damiba wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda, ya haifar da fushin sojin kasar, abinda ya jawo shima aka tsige shi a wannan shekarar, a wani juyin mulki karkashin Ibrahim Traore, wanda a yanzu shi ne shugaban kasar karkashin mulkin soja.

A farkon Wannan watan ne Burkina Faso ta sanar cewa ta dakile wani yunkuri na kashe shugaba Traore, da ake zargin Damiba ne ya shirya, wanda ya nemi mafaka a Lome, babban birnin kasar Togo.

Wani jami’in tsaro da wani dake da kusanci da shugaban kasar Togo sun shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters ranar Talata cewa An kama Damiba ranar Asabar, kuma An dauke shi a jirgi zuwa Ouagadougou, babban birnin Burkina Faso.

Togo ta tabbatar da fitar da Damiba daga kasar, inda ta ce ta yi haka ne, bisa bukata daga Burkina Faso.

Laifukan da ake tuhumar Damiba a Burkina Faso da su sun hada da almubazzaranci da wadaka da kudaden al’umma da halarta kudin haram, a cewar gwamnatin Togo

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama
Next Post: Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.