Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai
Published: December 11, 2025 at 9:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Amurka Donald ranar a laraba ya bayyana cewa Amurka ta kama wani jirgin dakon mai dake da takunkumi a kansa, a dab da gabar ruwan kasar Venezuela, matakin da ya janyo tashin farashin mai a kasuwannin duniya tare da kara wutar tankiya a tsakanin Amurka da Venezuela.

Wannan lamarin shine na farko a kan wani jirgin dakon man fetur da aka samu tun lokacin da Trump ya bada umurnin girke sojoji da makamai masu yawa a yankin.

Amurka tana kai hare-hare a kan kananan jiragen ruwan da tayi zargin cewa na safarar muggan kwayoyi ne, abinda ya sa ‘yan majalisa da kwararru a fannin shari’a suke nuna damuwa.

Antoni janar ta tarayyar Amurka, Pam Bondi, ta wallafa a shafin X cewa hukumar binciken manyan laifuffuka ta tarayyar Amurka, da hukumar tsaron cikin gida ta Amurka, da dogarawan gabar teku tare da tallafin sojoji sun aiwatar da takardar iznin kama wani jirgin ruwan dakon danyen mai da ake amfani da shi wajen jigilar man fetur da aka kafa ma takunkumi daga Venezuela da Iran.

Wani bidiyo na kasa da minti daya da Bondi ta wallafa ya nuna wasu jiragen helkwafta biyu sun doshi wani jirgin ruwa, inda aka ga dakaru dauke da makamai suna sauka ta igiyoyi a kan jirgin ruwan.

Jami’an gwamnatin Trump ba su fadi sunan wannan jirgin ruwan dakon mai ba, amma wani kamfanin sarrafa harkokin zirga zirgar jiragen ruwa na Britaniya mai suna Vanguard yace an kama jirgin ruwa mai suna Skipper a ranar laraba a gabar Venezuela.

Amurka ta sanya takunkumi acan baya a kan wannan jirgi, lokacin ana Kiransa da sunan Adisa, a saboda abinda amurka ta kira hannu dumudumu wajen safarar man kasar Iran.

Jirgin ruwan ya baro babbar tashar lodin mai ta kasar Venezuela a Jose tsakanin 4 da 5 ga watan nan na Disamba, a bayan da yayi lodin ganga miliyan daya da dubu dari daya na man Venezuela.

Farashin mai ya tashi a kasuwannin duniya a bayan da aka samu labarin kama wannan jirgin ruwa.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram!
Next Post: NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
Baital Malin Amurka Tace Sahannun Trump Zai Fito A Kudin Kasar Amurka
Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
  • CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.