Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi
Published: April 2, 2026 at 1:25 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutane goma sha uku sun mutu, yayin da wasu 57 suka jikkata sakamakon fashewar wasu ababe fashewa sanadiyyar matsalar wutar lantarki a wani sansanin sojoji na ƙasar Burundi a daren Talata, kamar yadda rundunar sojin ƙasar ta bayyana.

Mai magana da yawun sojojin Burundi, Gaspard Baratuza, ya shaida wa taron manema labarai a jiya Laraba cewa gidaje, gine-gine, motoci da kayan aikin soja sun lalace a sakamakon fashewar rumbun ajiyar makamai a Bujumbura, cibiyar kasuwancin ƙasar.

Wani mazaunin Bujumbura da ke zaune kusa da wurin yace fashe-fashen sun ɗauki sa’o’i da dama suna ci gaba.

Ya ce, “An shafe kusan sa’o’i shida ana ganin harsasai suna shawagi a sama suna sauka a wurare daban-daban.” Ya ƙara da cewa, “Mun dai tsaya a inda muke muna fakewa domin tsira,” kamar yadda ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters, inda ya nemi a sakaya sunansa.

A unguwar Musaga da ke kusa da sansanin sojin, wani mazauni ya ce ya ga wata budurwa ta faɗi ƙasa yayin da take gudu tare da wasu mutane. “Bayan ɗan lokaci ne na fahimci cewa bam ya bugi jikin ta da ƙarfi,” in ji shi, shi ma ya nemi a ɓoye sunansa.

Wani mutum kuma ya mutu jim kaɗan bayan an kammala taron addu’a a wata coci a unguwar Gasekebuye, kamar yadda wani mazaunin yankin ya bayyana.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya
Next Post: Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos

Karin Labarai Masu Alaka

Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.