Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya
Published: December 15, 2025 at 6:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sanda a kasar Australiya sun ce ‘yan bindigar da suka kashe mutane 15 a wurin wani bikin yahudawa a gundumar Bondi Beach dake bakin ruwa a Sydney, babban birnin kasar, wani uba ne da dansa.

An kashe uban mai shekaru 50 da haihuwa a wurin harin, yayin da dan nasa mai shekaru 24 ya ji mummunan rauni, yana kuma kwance a asibiti.

Jami’ai sun fadawa manema labarai a ranar litinin cewa harbe-harben na jiya na nuna kin jinin yahudawa ne.

‘Yan sanda suka ce har yanzu mutane 40 suna asibiti a bayan harin, cikinsu har da wasu ‘yan sanda biyu da suka ji mummunan rauni amma suna murmurewa.

‘Yan sandan suka ce mutane kimanin dubu 1 ne suka hallara a wani wurin shakatawa dake wannan bakin gabar ruwa da yayi suna domin murnar bukin yahudawa na Hanukkah.

A halin da ake ciki, mutanen Australiya suna yaba ma wani farar hula da aka gani a cikin hotunan bidiyo ya kama dan bindigar da kokuwa, suna mai bayyana shi a zaman mutumin da ya ceci rayukan mutane da yawa. Gidan telebijin na Channel 7, yace wannan farar hula, wani mutumi ne dan shekara 43 mai suna Ahmed al Ahmed, wanda ke da wani kantin sayarda kayan marmari.

Hotunan bidiyo da aka yada ta kafofin sada zumunci na Intanet, sun nuna Ahmed sanye da farar riga ya labe a bayan wata mota dake kusa, ya sulalo bayan dan bindigar ya kwace makamin daga hannunsa.

Wani dan’uwan wannan mutumin da shugabannin Australiya da na kasashen waje ke bayyanawa a zaman gwarzo, yace an harbi Ahmed a hannu da kuma a damtsensa sannan kuma Shi ma dan bindigar ya harbe shi har sau biyu, kuma yana asibiti an yi masa tiyata.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka
Next Post: Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.