Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya
Published: December 15, 2025 at 6:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sanda a kasar Australiya sun ce ‘yan bindigar da suka kashe mutane 15 a wurin wani bikin yahudawa a gundumar Bondi Beach dake bakin ruwa a Sydney, babban birnin kasar, wani uba ne da dansa.

An kashe uban mai shekaru 50 da haihuwa a wurin harin, yayin da dan nasa mai shekaru 24 ya ji mummunan rauni, yana kuma kwance a asibiti.

Jami’ai sun fadawa manema labarai a ranar litinin cewa harbe-harben na jiya na nuna kin jinin yahudawa ne.

‘Yan sanda suka ce har yanzu mutane 40 suna asibiti a bayan harin, cikinsu har da wasu ‘yan sanda biyu da suka ji mummunan rauni amma suna murmurewa.

‘Yan sandan suka ce mutane kimanin dubu 1 ne suka hallara a wani wurin shakatawa dake wannan bakin gabar ruwa da yayi suna domin murnar bukin yahudawa na Hanukkah.

A halin da ake ciki, mutanen Australiya suna yaba ma wani farar hula da aka gani a cikin hotunan bidiyo ya kama dan bindigar da kokuwa, suna mai bayyana shi a zaman mutumin da ya ceci rayukan mutane da yawa. Gidan telebijin na Channel 7, yace wannan farar hula, wani mutumi ne dan shekara 43 mai suna Ahmed al Ahmed, wanda ke da wani kantin sayarda kayan marmari.

Hotunan bidiyo da aka yada ta kafofin sada zumunci na Intanet, sun nuna Ahmed sanye da farar riga ya labe a bayan wata mota dake kusa, ya sulalo bayan dan bindigar ya kwace makamin daga hannunsa.

Wani dan’uwan wannan mutumin da shugabannin Australiya da na kasashen waje ke bayyanawa a zaman gwarzo, yace an harbi Ahmed a hannu da kuma a damtsensa sannan kuma Shi ma dan bindigar ya harbe shi har sau biyu, kuma yana asibiti an yi masa tiyata.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka
Next Post: Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira Labarai
Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai Wasanni
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.