Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai
Published: December 25, 2025 at 7:12 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 25, 2025

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a laraba yace kasar bani yahudun, zata kashe kudi dala bilyan 110 cikin shekaru hudu masu zuwa, wajen kafa sashen kera makamai maizaman kansa domin kasar ta rage dogaro kan wasu kasashe wajen samun makamai.

“Zamu ci gaba da neman wasu muhimman bukatu, a hanu daya kuma zamu samar da makamai da kan mu, inji PM Netanyahu a lokacinda yake magana a bikin kaddamar da shirin.

Bana cewa kasa zata iya biyawa kanta bukatunta kachokam ba, amma zamu yi bakin kokarin mu waje ganin haka. “in ji shi.

Burin mu shine gina sashen kera makamai na kasar Isara’ila domin mu rage dogaro kan kasashe ciki harda kawayen mu.

A gefe daya kuma, Isra’ila ta fada a Laraban nan cewa, zata dauki fansa bayan da ta zargi Hamas da keta yarjejeniyar tsagaita wuta, bayanda wani sojanta ya sami rauni sakamakon wata fashewa a Gaza, sai dai hamas ta musanta zargin, tana mai cewa, fashewar daga wani makami ne da aka bari a wurin tun lokacinda ake bata kashi.

PM Netinyahu ya ma baci lamarin ne da ya auku a Rafah, inda Isra’ilan take daukar matakan soji a yayinda yake magana a wani bikin yaye daliban makarantar horasda sojojin sama na kasar, ya kara da cewa Hamas ta fito fili ta nuna cewa ba zata kwance damara ba, kamar yadda yake kunshe cikin yarjejeniyar da aka kulla na tsagaita wuta  a cikin watan Oktoba.

A wani gefe kuma, yan share wuri zauna na Isra’ila a wani dan karamin wuri da ake kira Or Meir, sun bayyana a shafukan Telegram shirin su na ci gaba da korar Falasdinawa a yankin.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya
Next Post: Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
  • Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
  • Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.