Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar,
Published: January 1, 2026 at 10:31 AM | By: Bala Hassan

 Ƙasar Guinea kuma an zabi Mamady Doumbuya, madugun sojojin da suka yi juyin mulki a zaman shugaban kasa, kamar yadda kwarya-kwaryar sakamakon zabe da aka bayyana jiya talata, mataki da ya kammala shirin maido da kasar kan turbar demokuradiyya, ga kasar dake Afirka ta yamma da Allah Ya yiwa albarkar karfe. 

Tsohon kwamandan dakaru na musamman, wanda ake kiyasin dan shekaru 40 ne da haifuwa, Dumbouya ya yiwa shugaba Alpha Conde wanda yake shugabancin kasar tun 2010 juyin mulki shekara ta 2021. Juyin mulkin na kwango yana daga cikin jerin sauye sauye gwamnati da bakin bindiga har tara a kasashe da suke yammaci da kuma wadanda suke yankin tsakiyar Afirka daga shekara ta 2020.

Kwarya-kwaryar sakamakon zaben da aka bayar a  talata, ya nuna shugaba Doumbuya ya sami kashi 86.7 cikin dari na kuriu da aka kada, a zaben da aka yi ranar 28 ga watan Disemban 2025, rinjaye mai karfi da zata hana shi zuwa zagaye na biyu a zaben,

Tuni dai ake sa ran shugaba Doumbuya ya sami nasara a zaben, domin tsohon shugaban kasa Alpha Conde, da dadadden shugaban ‘yan hamayya Cellou Dalein Diallo suke gudun hijira, wadda ya baiwa shugaba Doumbuya damar fuskantar tsirarun ‘yan hamayya da suka kasa hada kai su takwas.

Kotun kolin kasar tana da kwanaki takwas ta tabbatar da sakamakon zaben, idan har akwai wadanda suke jayayya kan wannnan sakamako.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete
Next Post: Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro.

Karin Labarai Masu Alaka

Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
  • Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno Tsaro
  • Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.