Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba
Published: January 19, 2026 at 9:55 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron ya bayyana barazanar harajin da takwaransa na Amurka Donald Trump ya yi a matsayin abin da ba za su amince da shi ba, yana mai cewa babu barazanar da za ta tursasa ƙasashen Turai su yi abin da ba haka ba.

Shugaban na Faransa ya ci gaba da cewa, muddin Trump ya aiwatar da harajin da yake iƙirari, shakka babu za su mayar da martani, kuma cikin haɗin kai.

Wannan kalamai na Macron na zuwa ne, daidai lokacin da Firaministan Sweden, Ulf Kristersson ke bayyana cewa, babu wata ƙasa da ta isa ta tursasa su yin abin da basu yi niyya ba.

Yanzu haka dai ƙasar Jamus ta ce tana nazartar kalaman Mista Trump, kuma tuni ta fara tuntuɓar takwarorinta na Turai domin jin ina aka kwana a ragaya.

Kusan za a iya cewa dai kasashen Turai da alama matsayarsu ɗaya ce, domin itama Birtaniya ta bakin jagorar jam’iyyar Conservative, Kemi Badenoch ta ce sun karkata kan matsayar Firaministan ƙasar, tare da cewa suna goyon bayan al’ummar Birtaniya game da makomar yankin na Greenland.

Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142
Next Post: Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz Amurka
Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika
  • Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo Afrika
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.