UEFA Ta Shirin Janye Barazanar Kauracewa Gasar FIFA Yayin Da Italiya Ta Janye Goyon Bayanta Ga Infantino
Hukumar kula da kwallon kafa ta Turai, UEFA, na shirin janye barazanar da ta yi na kauracewa gasannin FIFA, bayan ta samu tabbacin cewa ba za a sake farfado da shirin sayar da kaso na gasannin Kofin Duniya da sauran manyan gasannin FIFA ga masu zuba jari masu zaman kansu ba.
Rahotanni sun ce UEFA ta samu wannan tabbaci ne yayin da Italiya ta zama sabuwar hukumar kwallon kafa ta kasa da ta janye goyon bayanta ga Shugaban FIFA, Gianni Infantino, a zaben shugaban hukumar da za a gudanar a watan Maris na shekara mai zuwa.
Hukumar Kwallon Kafa ta Italiya (FIGC) ta ce matakin nata na janye goyon bayan Infantino ya kasance ne domin bayyana matsayinta karara kan wasu sabbin matakan da shugaban FIFA ya dauka game da tafiyar da harkokin kwallon kafa da kuma ci gaban manyan gasannin kasa da kasa.
Matakin na UEFA ya samo asali ne daga wani shirin FIFA da ya tayar da kura a watan Yuli, wanda ya kunshi kafa wata sabuwar hukuma ta kasuwanci da kuma sayar da kaso 20 cikin 100 na hakkokin kasuwancin wasu manyan gasannin FIFA ga masu zuba jari masu zaman kansu.
Shirin ya fuskanci adawa daga dukkanin kungiyoyin kwallon kafa 55 da ke karkashin UEFA, wadanda suka amince da yiwuwar kauracewa gasannin FIFA idan aka ci gaba da shirin.
Sai dai yanzu, majiyoyin da ke sane da tattaunawar sun ce jami’an UEFA za su sanar da kwamitin zartarwa da shugabannin mafi yawan kungiyoyin kasashe mambobin ta cewa an cika sharuddan da suka kafa domin janye barazanar kauracewar.
UEFA ta bukaci abubuwa biyu: a janye shirin gaba daya, sannan a ba ta tabbacin cewa ba za a sake gabatar da irin wannan shiri a nan gaba ba.
Wata majiya da ke sane da tattaunawar ta ce matakin ba nasara ko rashin nasara ba ne ga UEFA, sai dai hanya ce ta kauce wa cutar da matasan ‘yan wasa da damar da suke samu na shiga manyan gasannin kasa da kasa.
A gefe guda kuma, matsin lamba na ci gaba da karuwa kan Infantino, yayin da UEFA, hukumar kwallon kafa ta Asiya (AFC) da CONCACAF ke tattauna yiwuwar kada kuri’ar rashin amincewa da shi gabanin zaben shugaban FIFA na watan Maris.
Infantino, wanda ke neman wa’adi na hudu a matsayin shugaban FIFA, har yanzu yana da goyon bayan kungiyoyin kwallon kafa na Afirka da Kudancin Amurka.
Sai dai wasu manyan jami’an kwallon kafa na Turai sun bayyana cewa makomar Infantino a FIFA na cikin hadari, yayin da ake kara samun kiraye-kirayen neman sauya tsarin tafiyar da hukumar.
Duk da rikicin, FIFA ta tabbatar da cewa dukkan kasashen da suka samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta mata ‘yan kasa da shekaru 20 da za a gudanar a Poland za su halarta, lamarin da ya rage fargabar cewa rikicin zai shafi gasannin FIFA nan take.


