Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar
Published: February 3, 2026 at 10:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talata, wakilan majalisar dokokin Phillipines suka yi zama domin yanke shawarar ko su ci gaba da sauraron karar neman tsige shugaban kasar Ferdinad Marcos Jr., wanda ake zargi da cin amanar kasa, rashawa, da kuma keta tsarin mulkin kasar.

Shugaba Marcos wanda yake tsakiyar wa’adin mulkinsa na shekaru shida, wanda ya musanta zargin, yana Fuskantar tuhuma da wani lauya dan gwagarmaya ya shigar gaban majalisar.

Idan har majalisa ta amince da zargin da ake yi wa shugaba Marcos, zai kasance shugaban kasar Phillipines na biyu da za’a tsige, na farko shine shugaba Joseph Estrada, wanda shari’arsa a shekara ta 2001 ta wargaje lokacin da wasu masu gabatar da kara suka fice daga inda ake shari’ar.

Laifuffukan da lauyan yake zargin shugaban na Phillipines sun hada da laifin sa a kama tsohon shugaban kasar Rodrigo Dutarte da mika shi ga kotun kasa da kasa mai hukunta manyan laifuffuka kan zargin da kotun take yi wa Dutarte na kashe duban mutane lokacin mulkinsa karkashin shirin yaki da miyagun kwayoyi.

Haka nan Marcos yana Fuskantar zarginsa kan yadda aka kashe dukiyar al’umma da ya kai ga abun fallasa kan ayyukan kare jama’a daga bala’in ambaliyar ruwa, da kuma zargin da ake yiwa shugaban kasar na mafani da miyagun kwayoyi, wadda idan ya tabbata ba zai cancanci ci gaba da shugabancin kasar ba.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar
Next Post: Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau

Karin Labarai Masu Alaka

Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • ‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
  • Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
  • Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.