Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11
Published: December 18, 2025 at 7:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Burkina Faso ta saki mayakan Najeriya su 11 wadanda ta tsare fiye da mako guda da ya shige, a bayan da jirginsu yayi saukar gaggawa.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, ya fada ranar alhamis cikin wata sanarwa ta kafar X cewa an warware batun matuka jirgin saman yakin Najeriya da mutanen dake cikin jirgin ta hanyar diflomasiyya.

Sanarwar ta ce gwamnatin mulkin soja ta Burkina Faso a karkashin jagorancin Ibrahim Traore, ta sako sojojin saman a bayan ganawa da wata tawagar Najeriya karkashin jagorancin Tuggar.

A makon da ya shige rundunar mayakan saman Najeriya ta ce jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Portugal domin sabis da aka saba yi ma jirage a lokacin da yayi saukar gaggawa a garin Bobo Dioulasso a yammacin Burkina.

Amma kuma gidan talabijin na kasar Burkina Faso ya watsa wani jawabin ministan harkokin wajen Najeriya Tuggar ranar laraba, inda yake cewa an bi ta hanyoyin da ba su dace ba wajen neman izinin wucewar jirgin ta samaniyar kasar, ya kuma nemi ahuwar hakan.

Shugaban gwamnatin mulkin soja ta kasar Mali, Janar Assimi Goita, ya ce saukar gaggawar da jirgin na Najeriya yayi, ya sa Kungiyar Kasashen Yankin Sahel ta sanya dakarun tsaron samaniyarta cikin shirin ko ta kwana, tare da ba su iznin harbo duk wani jirgin da ya shiga samaniyar yankin ba tare da izni ba.

Wannan kungiya ta kunshi kasashen Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar.

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce a yanzu matuka jirgin saman zasu wuce da shi wurin gyara a kasar Portugal.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Next Post: Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa

Karin Labarai Masu Alaka

Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.