Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: November 27, 2025 at 11:15 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 18, 2025

Hukumar lafiya ta duniya ta ayyana bijirewar cututtuka ga maganguna a matsayin babban al’amari dake kawo cikas da barazana a bangaren kiwon lafiyar jama’ah.
Najeriya dai ta kasance kasa ta 19 wajen rasa rayuka a cikin kasashe 204, kuma ana danganta mutuwar mutum dubu dari biyu da sittin da uku da dari hudu da matsalar Anti Microbial Resistance (AMR).
Dr. Muslim Bello Katagum yace AMR na nufin yadda cututtuka basa jin magani sakamakon shansu da ake yi ba bisa ka’ida ba.
Ganin yadda wannan matsala ke kara ta’azzara a duniya yasa Danida Alumni wato Dalibai da suka samu horo daga Danish International Development Agency, wato hukumar dake kula da cigaban kasashe ta kasar Denmark suka gudanar da taron a Abuja, domin watar da kan masu ruwa da tsaki da suka hada da NAFDAC, Standard Organisation Of Nigeria (SON), manoma, da sauransu domin tattauna hanyoyin wayar da kai don shawo kan matsalar AMR.
Sakataren Danida Alumni Nasiru Usman yace sun lura wannan matsala na daga cikin abubuwan dake damun Najeriya shiya suka shirya taron domin domin gwamnati ta kara maida hankali da sa ido kan lamarin.
Wakili daga Gonar Medogi Idris Usman Ibrahim yace taron ya kara fahimtar dasu yadda abun yake, inda ya kara da cewa a yanzu zasu maida hankali wajen bin ka’idar magani ga dabbobi da shuka.
Khadija Muhammad dake aiki da ma’aikatar kula da muhalli a sashen hana gurbacewar muhalli da kuma kula da lafiyar muhalli, jan hankali tayi wajen kula da tsaftar muhalli don gujewa cututtuka.
Matsalar AMR dai na daga cikin manyan matsaloli da hukumar lafiya ta duniya (WHO) tafi maida hankali akai a yanzu,ganin yadda matsalar ke haifar da salwantar rayuka da yaduwar cututtuka.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/AMR-GLOBAL-THREAT.mp3
Kiwon Lafiya, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum
Next Post: Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke

Karin Labarai Masu Alaka

Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
  • Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
  • Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.