Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: November 27, 2025 at 11:15 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 18, 2025

Hukumar lafiya ta duniya ta ayyana bijirewar cututtuka ga maganguna a matsayin babban al’amari dake kawo cikas da barazana a bangaren kiwon lafiyar jama’ah.
Najeriya dai ta kasance kasa ta 19 wajen rasa rayuka a cikin kasashe 204, kuma ana danganta mutuwar mutum dubu dari biyu da sittin da uku da dari hudu da matsalar Anti Microbial Resistance (AMR).
Dr. Muslim Bello Katagum yace AMR na nufin yadda cututtuka basa jin magani sakamakon shansu da ake yi ba bisa ka’ida ba.
Ganin yadda wannan matsala ke kara ta’azzara a duniya yasa Danida Alumni wato Dalibai da suka samu horo daga Danish International Development Agency, wato hukumar dake kula da cigaban kasashe ta kasar Denmark suka gudanar da taron a Abuja, domin watar da kan masu ruwa da tsaki da suka hada da NAFDAC, Standard Organisation Of Nigeria (SON), manoma, da sauransu domin tattauna hanyoyin wayar da kai don shawo kan matsalar AMR.
Sakataren Danida Alumni Nasiru Usman yace sun lura wannan matsala na daga cikin abubuwan dake damun Najeriya shiya suka shirya taron domin domin gwamnati ta kara maida hankali da sa ido kan lamarin.
Wakili daga Gonar Medogi Idris Usman Ibrahim yace taron ya kara fahimtar dasu yadda abun yake, inda ya kara da cewa a yanzu zasu maida hankali wajen bin ka’idar magani ga dabbobi da shuka.
Khadija Muhammad dake aiki da ma’aikatar kula da muhalli a sashen hana gurbacewar muhalli da kuma kula da lafiyar muhalli, jan hankali tayi wajen kula da tsaftar muhalli don gujewa cututtuka.
Matsalar AMR dai na daga cikin manyan matsaloli da hukumar lafiya ta duniya (WHO) tafi maida hankali akai a yanzu,ganin yadda matsalar ke haifar da salwantar rayuka da yaduwar cututtuka.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/AMR-GLOBAL-THREAT.mp3
Kiwon Lafiya, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum
Next Post: Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke

Karin Labarai Masu Alaka

Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kara Wa’adin Zaman Kurkuku A Senegal Ga Masu Auren Jinsi Afrika
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
  • Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.