Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke
Published: November 28, 2025 at 2:14 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kungiyar CISLAC guda cikin kungiyoyin rajin shugabanci na gari a Najeriya, ta bukaci gwamnatin kasar ta janye sunan Mr. Ayodele Oke daga jerin sunayen mutanen data mikawa majalisar dattawan kasar, domin ta amince a nada su jakadun kasashen ketare.

A jiya laraba ne, shugaba Tinubu ya mikawa majalisar sunan Alhaji Aminu Dalhatu daga jihar Jigawa da Mr. Kayode Are daga jihar Ogun da kuma Mr. Ayodele Oke daga jihar Oyo, wadanda yake muradin nadawa Jakadun Najeriya a ketare.

Sai dai, Kungiyar ta CISLAC, ta bukaci hukumar tsaro ta farin kaya DSS, kada ta wanke Mr. Oke saboda hukumar EFCC na tuhumar sa a gaban kotu, saboda zargin yana da hannu shi da mai dakinsa akan wasu kudade da hukuma ke zargin cewa, na almundahana ne.

A cikin watan Afrilu na shekara ta 2019, hukumar ta EFCC ta gano kudaden fiye da dala miliyan 43 da kuma Fam na Ingila fiye da miliyan 27 a qani gida dake kan titin Osborne a Unguwar Ikoyi ta birnin Lagos.

Bayan kammala bincike hukumar ta gabatar da batun a gaban babbar kotun tarayya dake Lagos, tana mai zargin cewa, Mr. Ayodele Oke da mai dakinsa nada hannu wajen boye kudaden.

Mr. Ayodele Oke dake zaman tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta Najeriya NIA, ya ki amsa sammacin kotu lokacin da hukumar EFFC ta gurfanar dashi domin amsa tuhuma akan wadancam kudade data gano.

Shugaban kungiyar ta CISLAC Auwal Musa Rafsanjani ya fadawa manema labarai a Abuja cewa, kungiyar ta kadu da yunkurin nada mutanen da ake tuhuma da rashawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin kunya ga kasa kuma ka iya tauye kimar Najeriya a idon duniya.

Yanzu dai Najeriya ta shafe fiye da shekaru biyu ke nan, bata da Jakadun dake kula mata da harkokin diplomasiyya a kasashen waje.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Next Post: Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora

Karin Labarai Masu Alaka

Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.