Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke
Published: November 28, 2025 at 2:14 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kungiyar CISLAC guda cikin kungiyoyin rajin shugabanci na gari a Najeriya, ta bukaci gwamnatin kasar ta janye sunan Mr. Ayodele Oke daga jerin sunayen mutanen data mikawa majalisar dattawan kasar, domin ta amince a nada su jakadun kasashen ketare.

A jiya laraba ne, shugaba Tinubu ya mikawa majalisar sunan Alhaji Aminu Dalhatu daga jihar Jigawa da Mr. Kayode Are daga jihar Ogun da kuma Mr. Ayodele Oke daga jihar Oyo, wadanda yake muradin nadawa Jakadun Najeriya a ketare.

Sai dai, Kungiyar ta CISLAC, ta bukaci hukumar tsaro ta farin kaya DSS, kada ta wanke Mr. Oke saboda hukumar EFCC na tuhumar sa a gaban kotu, saboda zargin yana da hannu shi da mai dakinsa akan wasu kudade da hukuma ke zargin cewa, na almundahana ne.

A cikin watan Afrilu na shekara ta 2019, hukumar ta EFCC ta gano kudaden fiye da dala miliyan 43 da kuma Fam na Ingila fiye da miliyan 27 a qani gida dake kan titin Osborne a Unguwar Ikoyi ta birnin Lagos.

Bayan kammala bincike hukumar ta gabatar da batun a gaban babbar kotun tarayya dake Lagos, tana mai zargin cewa, Mr. Ayodele Oke da mai dakinsa nada hannu wajen boye kudaden.

Mr. Ayodele Oke dake zaman tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta Najeriya NIA, ya ki amsa sammacin kotu lokacin da hukumar EFFC ta gurfanar dashi domin amsa tuhuma akan wadancam kudade data gano.

Shugaban kungiyar ta CISLAC Auwal Musa Rafsanjani ya fadawa manema labarai a Abuja cewa, kungiyar ta kadu da yunkurin nada mutanen da ake tuhuma da rashawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin kunya ga kasa kuma ka iya tauye kimar Najeriya a idon duniya.

Yanzu dai Najeriya ta shafe fiye da shekaru biyu ke nan, bata da Jakadun dake kula mata da harkokin diplomasiyya a kasashen waje.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Next Post: Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora

Karin Labarai Masu Alaka

Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • Jam’iyyar PDP Na Kara Tsunduma Cikin Mawuyacin Hali Shirye-Shirye
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.