Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke
Published: November 16, 2025 at 12:14 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Za’a buga wasan karshe tsakanin tawagar Super Eagles ta Najeriya da Leopards ta Jamhuriyar DR Congo.

Super Eagles ta Najeriya za su fafata da Leopards DR Congo a ranar Lahadi a wani wasa mai cike da kalubale, inda ake sa ran Afirka za ta fafata a wasan share fage na gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2026.

Super Eagles sun samu nasarar zuwa gasar karshe na share fage ta Afirka bayan sun yi nasara a kan Gabon (4-1) ita kuma DR Congo ta doke Kamaru (1-0).

A tarihi, wadannan kungiyoyi biyu sun kara da juna sau shida.

Jamhuriyar Congo ce ke kan gaba da ta samu nasara a wasani uku, inda Najeriya ta yi nasara a wasanni biyu, yayin da haduwa daya kawai ta kare da kunnen doki.

Cikakkun sakamakon fafatawar Najeriya da DR Congo

05/11/1966: Najeriya 3-2 DR Congo

26/11/1966: DR Congo 1-0 Najeriya

27/12/1966: DR Congo 1-0 Najeriya

03/03/2010: Najeriya 5-2 DR Congo

08/10/2015: Najeriya 0-2 DR Congo

28/05/2018: Najeriya 1-1 DR Congo

Wakilin Sashin Hausa na GTA Hausa ya tattauna da Kodineto na kungiyar Super Eagles Mr Pascal Patrick, da yake tare da tawagar ‘yan wasan, a kan  yadda ake ganin akwai ‘yan wasa biyu na Najeriya da baza su buga wasan ba.

Mai tsaron raga Stanley Nwabali yanzu ba a san ko zai buga ba, bayan ya ji rauni a wasan da Najeriya ta samu nasara kan Gabon da ci 4-1.

Shi kuwa mai tsaron raga Maduka Okoye na Udinese yana shirin maye gurbinsa. Dan wasa na biyu shine
Wilfred Ndidi dan wasan tsakiya bayan da ya samu katin gargadi. (Yellow card) guda biyu.

Mr. Patrick yace mahukunta a gasar sun tabbatar da cewa Wilfred Ndidi zai buga wasan, kuma hakan ya musu dadi.

Ya kara da cewa mai tsaron ragar Nwabali, ya halarci wani atisaye na wani bangare a ranar Asabar, yayin da sauran masu tsaron raga biyu, Okoye da Amas Obasogie, suka kammala atisayen su gaba daya.

Kocin Najeriya Eric Chelle yace, yana jiran cikakken rahoton likita kafin ya tabbatar ko Nwabali zai yi wasa da DR Congo.

GTA Hausa ta samu zantawa da dan wasan tsakiya na Super Eagles Alhasan Yusuf, inda ya bayyana mana karfin gwiwar samun nasara akan DR Congo, ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su taya su da addu’a.

‘Yan wasan da zasu buga wa DR Congo a cikinsu akwai, Aaron Wan‑Bissaka (West Ham United) mai tsaron baya na fukafikin hagu.

Inda yace zasu daura wajan samun nasara akan Najeriya, Wan-Bissaka yana karfafa tsaron DR Congo, inda ake ganin zai rage hanyoyin da Najeriya ta saba bi a gefen hagu.

Za’a buga wasan ne a ranar Lahadi 16 ga watan Nuwamban 2025, a babban Birnin Kasar Moroko.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Wasanni.mp3
Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025
Next Post: Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Nanata Aniyar Mallakar Greeland Daga Kasar Denmark Amurka
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.