Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana
Published: February 17, 2026 at 9:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin cikin gidan kasar Ghana ya bada labarin cewa ‘yan tawaye masu ikirarin Islama a Burkina Faso sun kashe ‘yan kasar Ghanan su bakwai masu cinikin tumatur, a lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari kan wani gari da ake kira Titao dake arewacin Burkina Faso a ranar Asabar data gabata.

Mutanen da harin ya rutsa da su, suna cikin wata tawagar mutum 18 da suka shiga makwabciyar kasar daga arewa, domin su sari tumatur, lokacin da mayakan suka aukawa garin, suka rarrabe maza da mata, daga bisani suka bude musu wuta, kamar yadda ministan ya gayawa wata tashar gidan rediyon kasar.

Minista Mohammed Mubarak Muntaka yace “suka goce da harbe harbe, suka kashe kusan dukkan maza da suke wurin, suka kona gawarwakin su da babbar motar da suke ciki,” har ba’za iya shaida su ba.

Minista Muntaka yace maza uku da mace daya sun tsallake rijiya da baya tare da samun raunuka. Saura mata bakwai dake cikin ayarin sun tsere ba tare da sun jikkata ba.

Daga bisani ya dauki hukumomi a Burkina Faso sa’o’i masu yawa suka sake kwato iko kan garin, kamar yadda ministan ya fada, ya kara da cewa, jami’an na Burkina Fason, sunyi alkawarin bada kariyan soja ga sauran tawagar da wadanda suka jikkata zuwa ofishin jakadancin Ghana dake birnin Ouagadougou, babban birnin kasar ta Burkina Faso.

Afrika, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya
Next Post: Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Gombe Ta Yi Kira Ga Jami’o’i Su Tallafa Wa Gwamnati Ta Hanyar Bincike Da Ƙirƙire-ƙirƙire Afrika
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
  • Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu Wasanni
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.