Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana
Published: February 17, 2026 at 9:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin cikin gidan kasar Ghana ya bada labarin cewa ‘yan tawaye masu ikirarin Islama a Burkina Faso sun kashe ‘yan kasar Ghanan su bakwai masu cinikin tumatur, a lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari kan wani gari da ake kira Titao dake arewacin Burkina Faso a ranar Asabar data gabata.

Mutanen da harin ya rutsa da su, suna cikin wata tawagar mutum 18 da suka shiga makwabciyar kasar daga arewa, domin su sari tumatur, lokacin da mayakan suka aukawa garin, suka rarrabe maza da mata, daga bisani suka bude musu wuta, kamar yadda ministan ya gayawa wata tashar gidan rediyon kasar.

Minista Mohammed Mubarak Muntaka yace “suka goce da harbe harbe, suka kashe kusan dukkan maza da suke wurin, suka kona gawarwakin su da babbar motar da suke ciki,” har ba’za iya shaida su ba.

Minista Muntaka yace maza uku da mace daya sun tsallake rijiya da baya tare da samun raunuka. Saura mata bakwai dake cikin ayarin sun tsere ba tare da sun jikkata ba.

Daga bisani ya dauki hukumomi a Burkina Faso sa’o’i masu yawa suka sake kwato iko kan garin, kamar yadda ministan ya fada, ya kara da cewa, jami’an na Burkina Fason, sunyi alkawarin bada kariyan soja ga sauran tawagar da wadanda suka jikkata zuwa ofishin jakadancin Ghana dake birnin Ouagadougou, babban birnin kasar ta Burkina Faso.

Afrika, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya
Next Post: Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
  • Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.