Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano
Published: December 16, 2025 at 6:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya janye shirin da ya yi na kafa wata Hisbah mai zaman kanta da ake kira Hisbah Fisabilillahi a Jihar Kano.

An bayyana wannan mataki ne cikin wata sanarwa da wani jigo a jam’iyyar APC a Kano, Dr. Baffa Babba Dan Agundi, ya fitar tare da sanya wa hannu.

A cewar sanarwar, matakin ya biyo bayan taron masu ruwa da tsaki da ya haɗa wakilai daga ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano. An gudanar da taron ne a Ofishin Kamfen na Tinubu.

Sanarwar ta bayyana cewa an yanke shawarar janyewa daga shirin ne bayan martanin jama’a da damuwar da aka nuna dangane da shirin kafa Hisbah mai zaman kanta.

Dama dai Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ne ya bada umarnin dakatar da shirin kafa Hisbar inda ya umarci jami’an tsaro su dau mataki kan masu shirin kafata a jihar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma
Next Post: Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.