Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar
Published: February 11, 2026 at 1:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka guda biyar daga jam’iyyar Republican sun gabatar da kudiri a majalisar wakilai ta ƙasar domin tilasta wa sakataren harkokin wajen Amurka gabatar da cikakken rahoto kan matakan da ƙasar ke ɗauka wajen magance zargin tsananta wa addini da kisan gilla da ake cewa na faruwa a Najeriya.

Idan kudirin ya zama doka, ana sa ran ma’aikatun harkokin waje da baitulmali na Amurka za su kakaba takunkumi, ciki har da hana biza da kwace kadarori, kan “mutane ko ƙungiyoyin da ke da hannu a take ‘yancin addini” a Najeriya.

Wadanda aka ambata a cikin kudirin domin yi musu takunkumi sun haɗa da tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) Miyetti Allah Kautal Hore da kuma waɗanda aka bayyana a matsayin “makiyayan Fulani masu ɗauke da makamai a Najeriya.”

Kudirin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan batun tsaro da rikice-rikicen addini a Najeriya.

Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga waɗanda aka ambata kan wannan mataki da aka gabatar a majalisar dokokin Amurka.

Amurka, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye Afrika
  • Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.