Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Published: December 9, 2025 at 6:51 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 9, 2025

Hukumomi a jamhuriyar Nijar sun umurci jami’an fiton kaya (Douanes) da su tsaurara binciken kayan da ke shigowa kasar daga Najeriya. Matakin wanda ke da nasaba da dalilan tsaro, wanda a ‘yan kwanaki kadan da suka shige aka samu tarin wasu ababe masu fashewa a wata motar jigila da ta tsallaka Nijar daga wata kasar waje. Tuni ‘yan kasuwa da kungiyoyin fararen hula suka fara bayyana matsayinsu a kai.

Ta hanyar wata takardar da ya aike wa mukarrabansa na illahrin jihohi ne shugaban hukumar Douanes na kasa Kanal Mohamed Yacouba Siddo ya umurce su da kara zuba ido kan kayayakin da ke shiga Nijar ta iyakar ta da Najeriya, abinda ke nufin daga yanzu za a sauke kayayakin da matakin ya shafa domin yi masu dai dai kafin samun izinin tsallakowa Nijar.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar Import Export Alhaji Yacouba Dan Maradi ya ce, matakin wanda a ka ayyana cewa abu ne da ke da nasaba da harakokin tsaro na zuwa ne a wani lokacin da alamu ke nuna yadda barazanar tsaro ke kara fadada a kasashen sahel da na yammacin Afirka, A ra’ayin shugaban kungiyar ci gaban karkara da birane Alhaji Ali Kalla matakin ya zo a kan gaba.

Koda yake a na danganta abin da yanayin tsaro wasu daga cikin mazauna garuruwan iyakar kasashen biyu na da fargaba game da yadda za a tafiyar da shi.

Iyakar Nijar da Najeriya mai tsawon kilo mita sama da 1500 na matsayin iyaka mafi mahimmanci ga kowacce daga cikinsu, kasancewarta gimshiki a harakokin tattalin arziki da cudanyar al’umomin kasashen biyu. jihohi a kalla 5 na Nijar ne ke makwaftaka da jihohi 7 na arewacin Najeriya.

TSAURARA BINCIKE A IYAKAR NIJAR NAJERIYA

 

Afrika

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro
Next Post: Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
An Kara Wa’adin Zaman Kurkuku A Senegal Ga Masu Auren Jinsi Afrika
Bayan Rikicin Manoma Da Makiyaya, Kwamitin White Paper Ya Ziyarci Bojude Da Kwami Afrika
Pads To Prosperity: NEDC Ta Horar Da Mata 280 Kan Kera Pads A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.