Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Published: December 9, 2025 at 6:51 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 9, 2025

Hukumomi a jamhuriyar Nijar sun umurci jami’an fiton kaya (Douanes) da su tsaurara binciken kayan da ke shigowa kasar daga Najeriya. Matakin wanda ke da nasaba da dalilan tsaro, wanda a ‘yan kwanaki kadan da suka shige aka samu tarin wasu ababe masu fashewa a wata motar jigila da ta tsallaka Nijar daga wata kasar waje. Tuni ‘yan kasuwa da kungiyoyin fararen hula suka fara bayyana matsayinsu a kai.

Ta hanyar wata takardar da ya aike wa mukarrabansa na illahrin jihohi ne shugaban hukumar Douanes na kasa Kanal Mohamed Yacouba Siddo ya umurce su da kara zuba ido kan kayayakin da ke shiga Nijar ta iyakar ta da Najeriya, abinda ke nufin daga yanzu za a sauke kayayakin da matakin ya shafa domin yi masu dai dai kafin samun izinin tsallakowa Nijar.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar Import Export Alhaji Yacouba Dan Maradi ya ce, matakin wanda a ka ayyana cewa abu ne da ke da nasaba da harakokin tsaro na zuwa ne a wani lokacin da alamu ke nuna yadda barazanar tsaro ke kara fadada a kasashen sahel da na yammacin Afirka, A ra’ayin shugaban kungiyar ci gaban karkara da birane Alhaji Ali Kalla matakin ya zo a kan gaba.

Koda yake a na danganta abin da yanayin tsaro wasu daga cikin mazauna garuruwan iyakar kasashen biyu na da fargaba game da yadda za a tafiyar da shi.

Iyakar Nijar da Najeriya mai tsawon kilo mita sama da 1500 na matsayin iyaka mafi mahimmanci ga kowacce daga cikinsu, kasancewarta gimshiki a harakokin tattalin arziki da cudanyar al’umomin kasashen biyu. jihohi a kalla 5 na Nijar ne ke makwaftaka da jihohi 7 na arewacin Najeriya.

TSAURARA BINCIKE A IYAKAR NIJAR NAJERIYA

 

Afrika

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro
Next Post: Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika
ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.