Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Published: December 9, 2025 at 6:51 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 9, 2025

Hukumomi a jamhuriyar Nijar sun umurci jami’an fiton kaya (Douanes) da su tsaurara binciken kayan da ke shigowa kasar daga Najeriya. Matakin wanda ke da nasaba da dalilan tsaro, wanda a ‘yan kwanaki kadan da suka shige aka samu tarin wasu ababe masu fashewa a wata motar jigila da ta tsallaka Nijar daga wata kasar waje. Tuni ‘yan kasuwa da kungiyoyin fararen hula suka fara bayyana matsayinsu a kai.

Ta hanyar wata takardar da ya aike wa mukarrabansa na illahrin jihohi ne shugaban hukumar Douanes na kasa Kanal Mohamed Yacouba Siddo ya umurce su da kara zuba ido kan kayayakin da ke shiga Nijar ta iyakar ta da Najeriya, abinda ke nufin daga yanzu za a sauke kayayakin da matakin ya shafa domin yi masu dai dai kafin samun izinin tsallakowa Nijar.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar Import Export Alhaji Yacouba Dan Maradi ya ce, matakin wanda a ka ayyana cewa abu ne da ke da nasaba da harakokin tsaro na zuwa ne a wani lokacin da alamu ke nuna yadda barazanar tsaro ke kara fadada a kasashen sahel da na yammacin Afirka, A ra’ayin shugaban kungiyar ci gaban karkara da birane Alhaji Ali Kalla matakin ya zo a kan gaba.

Koda yake a na danganta abin da yanayin tsaro wasu daga cikin mazauna garuruwan iyakar kasashen biyu na da fargaba game da yadda za a tafiyar da shi.

Iyakar Nijar da Najeriya mai tsawon kilo mita sama da 1500 na matsayin iyaka mafi mahimmanci ga kowacce daga cikinsu, kasancewarta gimshiki a harakokin tattalin arziki da cudanyar al’umomin kasashen biyu. jihohi a kalla 5 na Nijar ne ke makwaftaka da jihohi 7 na arewacin Najeriya.

TSAURARA BINCIKE A IYAKAR NIJAR NAJERIYA

 

Afrika

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro
Next Post: Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari Afrika
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
  • Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
  • Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • PDP Ta Koka Kan Rushe-rushe, Korar Gombawa Motors da Zaɓen Kananan Hukumomi A Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.