Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
Published: August 12, 2026 at 1:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitin 3G Taskforce ya ci gaba da aikin dasa bishiyoyi a gefen hanyoyin da ake ci gaba da aikinsu da kuma wadanda aka kammala a cikin birnin Gombe, inda aka gudanar da sabon aikin dasa bishiyoyi a kan sabuwar hanyar Gombe zuwa Bauchi.

Aikin ya shafi hanyar da ta taso daga Hedikwatar ‘Yan Sanda, ta bi ta Kwalejin Ilimi ta Tarayya, FCET, zuwa hanyar Mechanics Village, wadda aka mayar da ita tagwayen hanya.

Da yake jawabi jim kadan bayan kammala aikin, Shugaban Kwamitin kuma Mai Tula, Dakta Abubakar Atare Buba, ya ce shirin ya yi daidai da hangen nesan Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, na mayar da jihar cikin yanayi mai yawan ciyayi da bishiyoyi, tare da dakile matsalolin kwararowar hamada da zaizayar kasa.

Dakta Abubakar ya yi kira ga al’umma da su rungumi al’adar dasa bishiyoyi a yankunansu, tare da rokon mahukuntan FCET, tashar motoci ta Dankwanbo da kamfanin Gombe Line da su taimaka wajen kare bishiyoyin da aka dasa har zuwa lokacin da za su girma.

Shugaban Kwamitin ya yaba wa mambobin kwamitin da sauran jami’an da suka halarci aikin, bisa jajircewarsu da sadaukarwar da suka nuna wajen ganin an cimma nasarar shirin.

Ya bayyana cewa an sayo tare da kula da tsirrai da aka dasa domin bai wa kwamitin damar cimma adadin bishiyoyin da ya tsara dasawa.

Haka kuma, ya yabawa ofishin ACReSAL na jihar Gombe bisa goyon baya da kuma hadin gwiwar da yake bayarwa wajen aiwatar da shirin.

Wasu daga cikin masu wucewa da aka zanta da su, ciki har da Zainabu Mohammed da Musa Kanawa Yamaltu, sun bayyana shirin dasa bishiyoyin a matsayin abin da ya zo a kan lokaci, suna cewa zai taimaka wajen samar da muhalli mai tsafta, lafiya da kuma dacewa da rayuwar al’umma.

Afrika, Kimiya, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
Next Post: Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
Gwamnatin Tarayya Za Ta Sake Fasalin Shirin NYSC Afrika
Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika
Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • Anyi Jana’izar Mahaifiyar Nasiru El Rufai A Abuja Afrika
  • Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
  • Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.