Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC
Published: January 14, 2026 at 9:17 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kaddamar da shirin rajistar mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta hanyar zamani a jihar Gombe, karkashin jagorancin Gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Da yake kaddamar da shirin, Gwamna Inuwa Yahaya ya bukaci daukacin mambobin jam’iyyar da su koma mazabunsu domin yin rajistar yadda ya kamata ya kuma jaddada cewa mallakar Katin Zabe na Dindindin (PVC) da Katin Shaidar Dan Kasa (NIN) su ne muhimman sharuɗɗan samun cikakken rajista a jam’iyyar.

Gwamnan ya kuma yaba da irin namijin kokarin da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ke yi wajen ci gaban kasa da kuma karfafa matsayi da farin jinin jam’iyyar APC.

A nasa bangaren, Shugaban jam’iyyar APC na jihar Gombe, Nitte Amangal, ya tabbatar da cewa aikin rajistar zai gudana a dukkan mazabu 114 da ke fadin jihar, tare da bukatar mambobi su yi rajista a inda suka fito.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu
Next Post: Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.