Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC
Published: January 14, 2026 at 9:17 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kaddamar da shirin rajistar mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta hanyar zamani a jihar Gombe, karkashin jagorancin Gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Da yake kaddamar da shirin, Gwamna Inuwa Yahaya ya bukaci daukacin mambobin jam’iyyar da su koma mazabunsu domin yin rajistar yadda ya kamata ya kuma jaddada cewa mallakar Katin Zabe na Dindindin (PVC) da Katin Shaidar Dan Kasa (NIN) su ne muhimman sharuɗɗan samun cikakken rajista a jam’iyyar.

Gwamnan ya kuma yaba da irin namijin kokarin da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ke yi wajen ci gaban kasa da kuma karfafa matsayi da farin jinin jam’iyyar APC.

A nasa bangaren, Shugaban jam’iyyar APC na jihar Gombe, Nitte Amangal, ya tabbatar da cewa aikin rajistar zai gudana a dukkan mazabu 114 da ke fadin jihar, tare da bukatar mambobi su yi rajista a inda suka fito.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu
Next Post: Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
  • Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.