Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha Afrika
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH Afrika
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8 Afrika
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika

Zulum Ya Jinjinawa Hadiza Aliyu Kan Naɗin Ta A Matsayin Babbar Editar NAN
Published: August 30, 2026 at 9:56 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Borno a Arewa Maso Gabashin Najeriya Farfesa Babagana Umara Zulum, ya taya Hajiya Hadiza Mohammed Aliyu murnar naɗin da aka yi mata a matsayin mace ta farko da ta zama Babbar Edita (Editor-in-Chief) ta Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN).

Hadiza Aliyu, wadda ’yar asalin Jihar Borno ce, ita ce mace ta farko da za ta jagoranci sashen edita na NAN tun bayan kafuwar kamfanin sama da shekaru 40 da suka gabata.

Ta yi karatun Sadarwa da Harkokin Yaɗa Labarai (Mass Communication) a Jami’ar Maiduguri.

A cikin wata sanarwa da Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Dauda Iliya, ya fitar, Gwamna Zulum ya bayyana Hadiza Aliyu a matsayin ƙwararriyar editan labarai, mai ladabi, jajircewa da ƙwarewa, wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aiki a NAN.

Gwamna Zulum ya ce a madadin gwamnatin da al’ummar Jihar Borno, yana taya Hadiza Mohammed Aliyu murnar wannan babban matsayi da ta samu.

Ya bayyana jin daɗinsa da labarin naɗin nata, musamman kasancewarta shugabar tawagar editoci da ’yan jaridu sama da 500 da ke aiki a ofisoshin NAN daban-daban a faɗin ƙasar da kuma yankuna 18.

Gwamnan ya kuma buƙaci sabuwar Babbar Editar ta ci gaba da kare ƙa’idojin aikin jarida da suka sanya NAN ta zama amintacciyar kafar samun labarai.

Ya ƙara jaddada mata muhimmancin ci gaba da yaƙi da labaran ƙarya, bayanan yaudara, yaɗa bayanan ƙarya da kalaman ƙiyayya, musamman yayin da ƙasar ke tunkarar lokacin yakin neman zaɓe.

Gwamna Zulum ya yi mata fatan samun nasara a wa’adinta na mulki, tare da fatan za ta jagoranci harkokin kamfanin yadda ya kamata.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Yamai Cikin Rashin Tabbas Bayan Karar Harbe-Harbe Da Aka Ji
Next Post: Manoma Da Makiyaya: An Bukaci A Gaggauta Tantance Hanyoyin Shanu Da Iyakoki A Dukku

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
  • Kasashen Amurka Da China Sun Matsawa Ghana Domin Rage Kudaden Haraji Afrika
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
  • Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
  • Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.