Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka
Published: December 2, 2025 at 2:16 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Najeriya ta bada mafaka a ofishin jakadancinta ga wani dan hamayya a Guinea Bissau wanda yayi takarar shugaban kasa, mai suna Fernando Dias, bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar. Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ne ta bayyana haka a yau Litinin.

Wannan ayyanawar tana zuwa ne a dai dai lokacin da shugabannin kungiyar ECOWAS, karkashin jagorancin shugaban kasar Saliyo Julius Maada Bio, suka yi kokarin shawo kan sojojin da suka yi juyin mulkin da su janye juyin mulkin.

A wani taro da aka yi yau Litnin, inda aka fusata kamar yadda wani ganau na Reuters ya tabbatar, jami’an ECOWAS sun nemi sojojin su bari a bayyana sakamakon zaben shugaban kasar da aka yi, wanda ake gardama akai.

“ECOWAS ta bukaci da a dawo da tsarin demokuradiyya, da kuma ci gaba da tafiyar da harkokin zabe zuwa karshe,” inji ministan harkokin wajen Saliyo Musa Kabba.

Dan takarar shugaban kasar Dias mai shekaru 47 da haihuwa wanda sabon mutum ne a fagen siyasa, yace yana daf da lashen zaben kasar ne, sojoji suka yi juyin mulki a kasar.

Gungun jam’iyyun hamayya da suke goyon bayan Dias sun yi tur da juyin mulki, suna zargin tsohon shugaban kasar Embalo ne da hada baki da sojoji suka yi juyin mulki, don kada a bayyana sakamakon zaben.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu
Next Post: Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai

Karin Labarai Masu Alaka

Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anyi Asarar Biliyoyin Naira A Gobarar Kasuwar Singa Labarai
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
  • An Tura Rundunar Tsaron Sham Zuwa Kakarshin Ikon Kurdawa Labarai
  • RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.