Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane
Published: December 15, 2025 at 2:16 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 16, 2025

Hukumar NAPTIP, dake yaki da safara da fataucin bil’adama a Najeriya, ta dakile yunkurin wasu bata gari na safarar wasu yara su 11 ‘yan asalin jihar Jigawa a yankin arewa maso yammacin Najeriya. Hukumar tace tuni ta mika yaran da Jami’an ta suka kubutar ga majalisar karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Kwamandan hukumar a jihar ta Jigawa Abdulkadir Turajo ya fada yayin taron masu ruwa da tsaki a Dutse, shalkwatar jihar cewa, jami’an hukumar ta NAPTIP sunyi nasarar kubutar da yaran a birnin Lokoja na jihar Kogi yayin da ake kokarin kai su wani wurin da ba’a bayyana ba.

Yace yaran wadanda dukkanin su maza ne zalla, ‘yan shekaru 7 zuwa 15, an kwaso su ne daga kauyukan Tsaba da Kunkurawa da kuma Tsabare a karamar hukumar Ringim ta jihar ta Jigawa.

Kwamandan hukumar ta NAPTIP a Jigawa ya yabawa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar da kuma hadin kan da suka baiwa hukumar wajen sada yaran da iyayen su cikin hanzari.

Batun safarar yara kanana, galibi daga yankin arewaci zuwa kudancin Najeriya wani kalubale da hukumomin kasar ba su kai ga magance shi ba, duk da cewa, iyaye yara a yankin na arewacin Najeriya sun dade suna kokawa dangane da wannan matsala.

A shekarun baya baya nan, wannan matsala tayi kamari a Jihar Kano, jiha mafi yawan Jama’a a kasar, al’amarin daya kai ga hukumomin jihar sun kafa wani kwamitin bincike mai karfi domin lalubo hanyoyin dakile wannan matsala da galibi aka gano cewa, ana boye yaran ne jihohin Enugu da Abia bayan an yi safarar su daga Kano.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina
Next Post: Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki Afrika
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
  • Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.