Fiye da mata dubu shida daga sassan jihar Gombe ne suka halarci taron farko na Hadin Kan Mata da Ci Gaban Gombe, wanda Dr. Zainab Jamil Gwamna, matar ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar APC, Dr. Jamil Isyaku Gwamna, ta shirya.
An gudanar da taron ne a APC Square da ke Gombe, ƙarƙashin taken “Muryoyi Masu Ƙarfi, Mata Masu Haɗin Kai, Babban Tasiri”, inda mata daga dukkan ƙananan hukumomi 11 da yankunan raya ƙananan hukumomi 13 na jihar suka halarta.
Taron ya haɗa mata ‘yan kasuwa, ƙwararru, shugabannin al’umma, matan ‘yan takarar siyasa, masu kawo sauyi da sauran masu ruwa da tsaki, domin tattauna hanyoyin haɗa kan mata, ƙarfafa su da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa.
A yayin taron, mahalarta sun tattauna batutuwan da suka shafi jin daɗin mata, ƙarfafa hanyoyin taimakon juna, koyar da ‘yan mata, bunƙasa sana’o’i da kuma ƙara shigar mata cikin harkokin shugabanci da ci gaban tattalin arzikin jihar.
Da take jawabi, mai shirya taron, Dr. Zainab Jamil Gwamna, ta ce an shirya taron ne da nufin samar da wata ƙungiyar mata mai haɗin kai da manufa, wadda za ta tallafa wa juna tare da samar da damarmaki ga matasa.
Ta ce nasarar mace ɗaya ya kamata ta zama wata hanya ta buɗe ƙofa ga sauran mata, tana mai kira ga mata da su mayar da ilimi da ƙwarewar da suka samu cikin al’ummominsu.
Dr. Zainab ta buƙaci mata da su mayar da hankali wajen koyar da ‘yan mata, tallafa wa mata masu sana’o’i da ƙananan ‘yan kasuwa, ƙarfafa iyalai da kuma ba da gudummawa wajen ci gaban al’umma.
Ta kuma yaba wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, kan shirye-shiryen gwamnatinsa da suka shafi mata da matasa, tare da gode wa mijinta, Dr. Jamil Isyaku Gwamna, bisa goyon bayan da yake ba ta wajen gudanar da ayyukan da suka shafi ci gaban mata da jihar.
A nata ɓangaren, matar Gwamnan Jihar Gombe, Dr. Asma’u Muhammadu Inuwa Yahaya, ta yaba da shirin tare da bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama da za ta ƙara haɗa kan mata daga sassa daban-daban na jihar.
Dr. Asma’u ta ce mata muhimman abokan hulɗa ne wajen ci gaban iyalai, al’umma da jihar baki ɗaya, tana mai jaddada cewa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya za ta ci gaba da tallafawa shirye-shiryen da za su inganta rayuwar mata da matasa.
Ta kuma yi kira ga mata da su ci gaba da nuna haɗin kai, taimakon juna da amfani da damar da suke da ita wajen bayar da gudummawa ga ci gaban al’umma.
Wasu daga cikin masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun bayyana shi a matsayin wani gagarumin mataki wajen haɗa kan mata da bunƙasa matsayinsu a Jihar Gombe.
Sun ce dimbin mahalartan taron ya nuna irin ƙarfin da mata suke da shi idan suka haɗa kai kan manufa guda, tare da jaddada muhimmancin haɗin gwiwa, koyar da juna, dogaro da kai da kuma ƙara shigar mata cikin harkokin ci gaban al’umma da shugabanci.
Mahalarta taron sun bayyana fatan cewa tasirin taron ba zai tsaya a ranar taron kaɗai ba, sai dai zai haifar da ƙulla kyakkyawar alaƙa tsakanin mata, ƙarfafa dogaro da kai da kuma zaburar da mata da ‘yan mata wajen taka rawa wajen gina makomar iyalansu da al’ummominsu.
An rufe taron ne da kira ga mata a faɗin Jihar Gombe da su ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai, taimakon juna da kuma mayar da ilimi da alaƙar da suka samu a taron zuwa ayyukan da za su amfani al’ummominsu.
Masu ruwa da tsaki sun kuma ce irin wannan taro ya nuna damar da mata suke da ita wajen ba da gudummawa ga ci gaban jihar, tare da bayyana cewa haɗin kan da aka nuna zai iya ƙara wa ‘yan takarar jam’iyyar APC ƙarfi a babban zaɓen shekarar 2027.


