Hukumar Kula da Agajin Gaggawa ta jihar Gombe (GOSEMA) ta kammala horon ƙara wa juna sani na kwanaki uku ga mambobin Kwamitocin Kula da Agajin Gaggawa na Ƙananan Hukumomi (Local Emergency Management CommitteesvLEMCs), da nufin ƙarfafa shirye-shiryen tunkarar bala’o’i da inganta ayyukan ba da agajin gaggawa a faɗin jihar.
An gudanar da horon ne ƙarƙashin jagorancin Babban Sakataren GOSEMA, Alhaji Haruna Abdullahi Haruna (Bacoza), inda aka tsara shi zuwa matakai uku domin bai wa mambobin kwamitocin daga dukkan ƙananan hukumomi goma sha ɗaya damar halarta, bisa shiyyoyin Gombe ta Arewa, Gombe ta Tsakiya da Gombe ta Kudu.
A jawabin da ya gabatar a buɗe taron da kuma lokacin rufe shirin, Babban Sakataren GOSEMA ya yaba wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa goyon baya da kyakkyawan yanayin aiki da ya samar wa hukumar, wanda ya ba ta damar gudanar da ayyukan kare rayuka da dukiyoyin al’umma yadda ya kamata.
Alhaji Haruna Bacoza ya bayyana cewa kowace ƙaramar hukuma a Najeriya tana da Kwamitin Kula da Agajin Gaggawa wanda Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma ke jagoranta tare da sauran mambobi.
Ya ce kwamitocin na da muhimmiyar rawa wajen gano haɗurran da ka iya afkuwa, wayar da kan jama’a da kuma haɗa kai da hukumomin agajin gaggawa wajen ɗaukar matakan kariya.
Ya buƙaci mahalarta taron su koma yankunansu su isar da ilimi da dabarun da suka samu ga sauran mambobin kwamitocinsu da al’ummominsu domin ƙarfafa shirin tunkarar bala’o’i, rage asarar rayuka da dukiyoyi da kuma gina al’ummomi masu juriya.
A tsawon kwanaki ukun horon, ƙwararru daga GOSEMA, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Gombe da Ƙungiyar Red Cross ta Najeriya sun gabatar da muƙalu kan muhimman fannoni na kula da bala’o’i.
Daga cikin muƙalun akwai Tsarin Gargaɗin Farko na Bala’o’i a Matakin Al’umma, Taswirar Haɗurra a Matsayin Muhimmin Kayan Aikin Gudanar da Haɗarin Bala’o’i, Shirye-shiryen Tunkarar Bala’o’i da Tsare-tsaren Ba da Agajin Gaggawa, Hanyoyin Rage Haɗarin Gobara da Kare Kai a Matakin Al’umma, da kuma Gabatarwa ga Agajin Farko da Kula da Gaggawa.
Masu gabatar da darussan sun jaddada muhimmancin taswirar haɗurra, tsarin gargaɗin farko, shirye-shiryen tunkarar bala’o’i, saurin ba da agajin gaggawa, kariya daga gobara, ilimin agajin farko da haɗin kan al’umma wajen rage illolin bala’o’i.
Sun kuma yabawa sarakunan gargajiya, shugabannin al’umma da ƙungiyoyi masu zaman kansu bisa gudummawar da suke bayarwa wajen wayar da kai da hidimtawa al’umma.
Horon ya gudana cikin tattaunawa mai armashi, inda mahalarta daga dukkan ƙananan hukumomin jihar suka gabatar da tambayoyi, suka bayyana ƙalubalen da suke fuskanta a yankunansu tare da musayar ƙwarewa kan hanyoyin inganta shirin tunkarar bala’o’i.
GOSEMA ta bayyana cewa horon na daga cikin dabarun gwamnatin Jihar Gombe na gina ingantaccen tsarin gudanar da harkokin agajin gaggawa a matakin ƙasa da ƙasa, tare da tabbatar da cewa kowace al’umma ta samu ilimi da ƙwarewar da za su taimaka wajen rage haɗarin bala’o’i da kare rayuka da dukiyoyi.


