Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ƙarin albashi ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce na inganta jin daɗin jami’an tsaro da ƙarfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.
Sanarwar da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ta bayyana cewa kimanin jami’ai da sojoji 250,000 ne za su amfana da sabon tsarin albashin, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Satumban 2026.
A cewar sanarwar, jami’an da ke daga mukamin Birgediya Janar zuwa Janar za su samu ƙarin albashi na kashi 30 cikin ɗari. Waɗanda ke daga mukamin Kanal zuwa Warrant Officer kuma za su samu ƙarin kashi 50 cikin ɗari, yayin da sojojin da ke daga mukamin Private zuwa Staff Sergeant za su amfana da ƙarin albashi mafi girma na kashi 80 cikin ɗari.
Sabon tsarin albashin zai ƙara yawan kuɗin da gwamnatin tarayya ke kashewa kan albashin jami’an rundunar sojin daga naira biliyan 660 zuwa naira biliyan 924 a shekara.
Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa na yaba wa jajircewa da sadaukarwar jami’an rundunar sojin wajen yaƙi da matsalolin tsaro da suka haɗa da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan ƙasar.
Ya ce jami’an tsaro sun cancanci tallafi da yabo saboda rawar da suke takawa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗinsu tare da samar musu da makamai da fasahohin zamani domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.
Shugaban ƙasar ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta iya samun ci gaba mai ɗorewa ba tare da ingantaccen tsaro ba, yana mai cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da amfani da dukkan rundunonin tsaro wajen yaƙi da barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya.
A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya buƙaci jami’an rundunar sojin da su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin alamar godiya daga gwamnati, tare da bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa Najeriya za ta yi nasara kan masu neman tada zaune tsaye da tarwatsa zaman lafiyar ƙasar.


