Ƙungiyar Ma’aikatan Jinyar Yara ta Najeriya (NANPAN), reshen jihar Gombe, ta ƙara ƙaimi wajen wayar da kan al’umma kan muhimmancin shayar da jarirai nono kaɗai a matsayin wata muhimmiyar hanya ta inganta lafiyar uwa da jariri.
An gudanar da gangamin wayar da kan ne a ƙarƙashin taken “Shayar da Jarirai Nono Domin Samar da Kyakkyawar Fara Rayuwa,” inda aka ilmantar da mata masu juna biyu da masu shayarwa kan amfanin shayar da jarirai nono kaɗai daga haihuwa har zuwa cikar watanni shida.
Da take jawabi yayin shirin, Mai Kula da NANPAN a jihar Gombe, Rashidat Abubakar, ta bayyana cewa shayar da jarirai nono kaɗai daga haihuwa zuwa watanni shida na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da lafiyar yara, girma mai kyau da bunƙasar ƙwaƙwalwarsu. Ta yi kira ga iyaye mata da iyalai su rungumi wannan kyakkyawan ɗabi’a domin kare lafiyar ‘ya’yansu.
Ta ce nonon uwa na ɗauke da dukkan sinadaran gina jiki da jariri ke buƙata a cikin watanni shida na farko na rayuwarsa, ba tare da buƙatar ba shi ruwa ko wani nau’in abinci ba.
Sauran mambobin ƙungiyar, da suka haɗa da Mariya Isah Bello, Loveth Emevo da Hajara Borno Lawal, sun bayyana cewa shayar da jarirai nono kaɗai na ƙarfafa garkuwar jiki, kare yara daga kamuwa da cututtuka, inganta girma da kuma bunƙasa ƙwaƙwalwarsu.
A yayin gangamin wayar da kan da aka gudanar a Asibitin Haihuwa na Gidan Magani da kuma Asibitin Mata da Yara na Zainab Bulkachuwa, ƙwararrun ma’aikatan lafiya Jamila Haruna Adamu da Amina Haruna sun shawarci mata masu juna biyu da su guji shan magunguna ba tare da umarnin likita ba, sannan su fara shayar da jariransu nono nan take bayan haihuwa.
Sun jaddada cewa ya kamata a ci gaba da bai wa jariri nonon uwa kaɗai har tsawon watanni shida ba tare da ba shi ruwa ko wani nau’in abinci ba, domin nonon uwa ya ƙunshi dukkan abubuwan gina jiki da jariri ke buƙata.
Masanan lafiyar sun kuma yabawa gwamnatin mai ci saboda irin goyon baya da take bai wa shirye-shiryen kula da lafiyar uwa da jariri, lamarin da suka ce na taimakawa wajen inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.
A nata jawabin, Mai Kula da Asibitin Haihuwa na Gidan Magani, Zainab Umar Chiroma, tare da Mai Kula da Asibitin Mata da Yara na Zainab Bulkachuwa, Florence Emmanuel, sun yabawa NANPAN bisa zaɓen cibiyoyinsu domin gudanar da gangamin wayar da kan. Sun bayyana shirin a matsayin wanda ya zo a kan lokaci kuma zai taimaka wajen ƙara wayar da kan mata kan muhimmancin shayar da jarirai nono kaɗai.
Ƙungiyar NANPAN ta sake jaddada aniyarta na ci gaba da wayar da kan al’umma game da muhimmancin shayar da jarirai nono kaɗai, tare da yin kira ga gwamnati, ma’aikatan lafiya, shugabannin al’umma da iyalai da su ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen da ke inganta lafiyar uwa da jariri.


