Papa Roma Leo, ya fadawa kamfanin dilancin labarai na Reuters cewa zai ci gaba da suka kan dukkan wani matakin yaki, bayanda shugaba Donald Trump ya caccaki shugaban darikar katholika mai mabiya bilyan daya da milyan dari hudu a fadin duniya.
A kalamai da yayi cikin jirginsa kan hanyar sa ta zuwa birnin Algiers, inda ba Ameriken Papa Roman zai fara ziyarar aiki na kwana 10 zuwa kasashen Afirka hudu, shugaban darikar katholikan yace ana wargi da koyawar masihanci.
“Bana so mu shiga muhawara dashi, Leo ya gayawa Reuters, yayinda yake gaida ‘yan jarida da suke tare da shi, “Bana jin sakon addinin kirista abun wasa bane, kamar yadda wasu mutane suke yi.”
“Zan ci gaba da magana da babban muriya kan yaki, da nufin wanzar da zaman lafiya, da tuntubar juna, da mu’amala tsakanin kasashe, domin samun hanyoyin warware matsaloli, inji PapaRoma a magana da yayi cikin harshen turanci.
“Mutane masu yawan gaske suna wahala sosai a duniya a yau,” inji Papa Roma Leo, ana kashe mutane masu yawan gaske wadanda basu aikata laifin komi ba, saboda haka nake gani akwai bukatar wani ya tashi tsaye domin acewarsa, akwai wata hanya da ta fi dacewa.
Sakon coci, da sakona, da sakon linjila shine, “Allah ya sanya albarka ga masu wanzar da zaman lafiya. Bana kallon matsayina a zaman siyasa ko dan siyasa, inji Papa Roma Leo.
Papa Roma Leo, wanda dan asalin birnin Chicago ne a Amurka, ya kasance babban mai sukar yakin Amurka da Isra’ila kan Iran a makonnin baya bayan nan.
Abunda yasa shugaba Trump ya caccaki shi a zaman martani kan sukar da Papa Roman yake kan yakin na gabas ta tsakiya.


