Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON)
Published: December 2, 2025 at 6:45 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 2, 2025

Mai tsaron ragar ƙungiyar kwallon kafa ta Kamaru Andre Onana ya sake fuskantar wani mummunan rauni hakan yasa aka cire shi daga tawagar Kamaru da za ta fafata a gasar cin kofin kasashen Afirka da ke tafe.

Dan wasan mai shekaru 29 ya sha wahala a kakar wasa ta 2025-26, bayan ya rasa matsayinsa na mai tsaron raga na 1 a Manchester United kafin aka ba shi damar komawa kungiyar Trabzonspor ta Turkiyya a matsayin aro na tsawon kakar wasa a watan Satumba.

Ba a saka Onana a cikin jerin ‘yan wasa masu tsaron raga hudu ba duk da cewa Kamaru ta zabi ‘yan wasa hudu.

An yi ta jan ido a ranar Litinin lokacin da Kamaru ta fitar da ‘yan wasa 28 da za su fafata a AFCON, wanda za a fara a ranar Lahadi, 21 ga Disamba in da Morocco mai masaukin baki za ta fafata da Comoros.

Duk da zabar masu tsaron gida hudu, Onana bai shiga cikin jerin ‘yan wasan Indomitable Lions ba.

‘Yan wasa biyu da aka sanya a cikin tawagar sune dan wasan gaba na United Bryan Mbeumo da dan wasan tsakiya na Brighton & Hove Albion Carlos Baleba, wanda aka alakanta da komawa Old Trafford a lokacin bazara.

Tsohon ɗan wasan gefe na Tottenham Hotspur Georges-Kevin Nkoudou – wanda yanzu yake bugawa ƙungiyar Diriyah Club ta Saudiyya wasa – shi ma ƙasarsa ta zaɓe shi.

A hukumance: Tawagar ‘yan wasa 28 na Kamaru wadanda ba su hada da Onana ba

Tawagar Kamaru ta 2025 AFCON:

Masu tsaron gida: Devis Epassy, ​​Simon Omossola, Simon Ngapandouetnbu, Edouard Sombang

Masu tsaron baya: Samuel Junior Kotto, Gerzino Nyamsi, Jean-Charles Castelletto, Nouhou Tolo, Flavien Enzo Boyomo, Nagida Mahamadou, Junior Tchamadeu, Christopher Wooh, Darlin Yongwa

‘Yan wasan tsakiya: Martin Ndzie, Carlos Baleba, Arthur Avom, Eric Junior Dina Ebimbe, Fidel Brice Ambina, Danny Namaso, Christian Bassogog, Georges-Kevin Nkoudou, Jean Junior Onana, Olivier Kemen

Masu wasan gaba: Bryan Mbeumo, Christian Kofane, Frank Magri, Karl Etta Eyong, Patrick Soko.

Hukumar Kwallon Kafa ta Kamaru ta kori kocin da ya lashe gasar AFCON sau biyar a rana ɗaya.

 

Hukumar Kwallon Kafa ta Kamaru – karkashin jagorancin tsohon dan wasan Barcelona, Chelsea da Inter Milan Samuel Eto’o – ta salami mai horaswa Marc Brys a ranar da aka sanar da sunayen ‘yan wasan da zasu  fafata mata a gasar cin kofin kasashen Afirka AFCOB

Inda suka nada David Pagou a matsayin wanda zai maye gurbin Brys, kasar Kamaru za su fafata da Gabon a wasan farko cikin makonni uku kacal (24 ga Disamba). Kamaru kuma za ta fafata da Ivory Coast (28 ga Disamba) da Mozambique (31 ga Disamba) a matakin rukuni.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1
Next Post: Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu

Karin Labarai Masu Alaka

Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
  • Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.