Daga Masanin Harkokin siyasa a Najeriya kuma Mai sharhi akan al’amuran yau da kullum Ferfesa Rufai Ahmed Alkali:-
Zaben gwamnan jihar Osun da aka gudanar a makon da ya gabata ya zo ya wuce, amma sakamakonsa ya bar baya da ƙura, inda ya haifar da muhawara da ce-ce-ku-ce tsakanin ’yan siyasa, kafafen yaɗa labarai, musamman kafafen sada zumunta, da kuma masu bibiyar harkokin siyasa.
Abin takaici, duk da cewa ba abin mamaki ba ne, mafi yawan masu sharhi sun fi mayar da hankali ne kan abin da suka bayyana a matsayin faduwar APC a hannun Accord Party, wadda ƙaramar jam’iyya ce.
A cikin wannan hayaniyar, da yawa sun kasa duba babban abin da sakamakon zaben ke nufi.
Na farko, gaskiya ne cewa Accord Party ta lashe zaben da kuri’u 511,067.
Sai dai APC ita ma ta samu kuri’u 444,815, adadin da ya fi yawan kuri’un da ta samu a zaben gwamnan Osun na shekarar 2022, inda ta samu kusan 403,000. Wannan na nufin APC ta samu ƙarin kuri’u sama da kashi 18 cikin 100 idan aka kwatanta da zaben 2022.
Na biyu, idan aka kwatanta kuri’un APC guda 444,815 da jimillar kuri’u 1,010,684 da aka kada, APC ta samu kusan kashi 44.01 cikin 100 na dukkan kuri’un da aka kada a zaben Osun.
Wannan muhimmin abu ne idan aka yi la’akari da zaben shugaban ƙasa, domin ɗaya daga cikin muhimman sharuddan lashe zaben shugaban ƙasa shi ne samun aƙalla kashi 25 cikin 100 na kuri’un da aka kada a jiha. A wannan yanayin, APC ta samu fiye da abin da ake bukata a Osun.
Na uku, wani muhimmin batu da mafi yawan masu sharhi suka yi watsi da shi shi ne cewa Accord Party ba ta da ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben 2027.
Haka kuma, Gwamna Ademola Adeleke ya riga ya bayyana aniyarsa ta mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya.
Ko da yake siyasa tana cike da abubuwan mamaki, ba abu ne mai sauƙin tsammani ba cewa Gwamna Adeleke zai sauya matsayinsa, ya yi watsi da Shugaba Tinubu, sannan ya koma ya mara wa wata hamayyar siyasa da ke fama da rarrabuwar kai baya.
Na huɗu, babu shakka, ADC ce ta fi kowa yin mummunan sakamako a zaben Osun.
Wannan lamari ne mai matuƙar muhimmanci, amma bai samu kulawar da ya kamata ba daga masu sharhi da kafafen yaɗa labarai.
Ɗan takarar ADC, Najeem Salaam, ya samu kuri’u 17,180 kacal. Wannan adadin ma ya yi ƙasa da kuri’u 18,600 da ɗan takarar APC ya samu a ƙaramar hukumar Ife East kaɗai.
Abin da ya ƙara sanya wannan sakamako ya zama abin mamaki shi ne cewa Najeem Salaam tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Osun ne.
Na biyar, wannan sakamako ya fi zama abin lura saboda ADC ta samu gagarumar damar bayyana kanta a matakin ƙasa yayin yakin neman zaben.
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar, da kansa ya je Osun domin yi wa Najeem Salaam kamfen.
Haka kuma, Rauf Aregbesola, tsohon gwamnan Osun na wa’adi biyu kuma Babban Sakataren ADC na ƙasa, ya jagoranci wani ɓangare na yaƙin neman zaɓen jam’iyyar a jihar.
Duk da wannan gagarumar fitowar jam’iyyar a idon ƙasa, ADC, wadda ke ikirarin kasancewa “Ƙarfi na Uku”, ta samu mafi ƙarancin kuri’u, inda ta zo matsayi na uku da tazara mai yawa.
Darasin da ke cikin wannan sakamako shi ne cewa sunan jam’iyya a matakin ƙasa, yawan surutu a kafafen yaɗa labarai da kuma fitowar manyan ’yan siyasa ba su isa su tabbatar da ƙarfin jam’iyya a matakin jiha ba.
Sai an samu ingantaccen tsarin siyasa da karɓuwa a tsakanin masu zaɓe.
A fili yake cewa rashin nasarar ADC a Osun babban gargadi ne ga jam’iyyar, musamman idan tana da burin samun gagarumar nasara a zaɓukan ƙasa baki ɗaya a shekarar 2027.
Tabbas, zaben Osun darasi ne ga dukkan jam’iyyun siyasa. Kuma ga APC, sakamakon zaben ya kamata ya zama wata dama ta nazari, gyara kura-kurai da kuma ƙara ƙarfafa dabarunta kafin babban zaben 2027.


