Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal
Published: February 25, 2026 at 12:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Prime ministan kasar Senegal, Ousmane Sonko ya nemi a dabbaka dokar da zata ninka zama gidan kurkuku daga shekara 5 zuwa 10 ga duk wadanda aka kama da yin auren jinsi, da sauran abubuwa da suka jibanci irin wannan halayya.

Da yake jawabi ga majalisar kasar a ranar Talata, Sonko ya ce, dokar zata shafi duk wata dangantaka da bata dace ba tsakanin jinsin mutane daya, kuma duk wanda aka kama yana irin wannan alaka da wanda bai kai shekaru 21 ba, zai fuskanci cikakken hukunci.

Wadanda aka kama da laifi kuma zasu iya fuskantar tara daga sefa miliyan biyu zuwa miliyan 10 wanda yayi daidai da dala 3,590 zuwa dala 17,953.

Sonko yayi kira ga ‘yan majalisar kasa daga kowacce jam’iyya da su goyi bayan dokar, ya kuma zargi kasashen yamma da tallata goyon baya ga ‘yancin masu auren jinsi a Senegal, da kuma jawo rudanin siyasa.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki
Next Post: Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa Afrika
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
  • Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.