Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha
Published: January 17, 2026 at 10:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi tayin sasanta rigimar dake tsakanin kasashen Masar da Habasha game da rikicin kogin Nile da ya ratsa kasashen biyu.

Trump ya ce a shirye yake da ya shiga tsakani domin kawo karshen takaddama kan yadda rabon ruwan kogin Nile ze kasance tsakanin kasashen biyu ta hanyar da ta dace, a wata takarda da ya aikewa shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi, wadda kuma aka wallafa a shafin sa na Truth social.

Kaddamar da wani babban madatsan ruwa da kasar fadar gwamnati a Addis Ababa ta yi ranar 9 ga Watan Satumbar bara ya jawo fushin fadar gwamnatin Cairo dake kasa daga kogin Nile.

Habasha, wadda ita ce ta biyu a mafi yawan mutane, a nahiyar Afirka, da suka kai fiye da miliyan 120, na ganin dam din da ta gina zai taka muhimmiyar rawa wajen tattalin arzikin kasar.

Masar kuma a nata bangaren ta ce dam din ya sabawa yarjejeniyar kasa da kasa, kuma zai iya jawo fari da ambaliyar ruwa duka, Habasha ta ki amincewa da hakan.

Trump ya yabawa Sisi a baya, har ya zuwa lokacin da ya je Masar a watan Oktoba domin sa hannu kan yarjejeniyar da ta Shafi rikicin Gaza.

Da ya ke tsokaci game da abin, Trump ya maimaita damuwar da fadar gwamnatin Cairo ke da shi game da maganar ruwan.

Amurka

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato
Next Post: Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Trump Yace Kawayen Amurka A Kungiyar NATO Basa Goyon Bayan Su Afrika
Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.