Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar
Published: December 24, 2025 at 2:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jamhuriyar Nijar ta kudiri aniyar rage yawan shinkafa da masara da alkamar da ke shiga kasar daga ketare da kashi 50% kafin nan da shekarar 2027.

Gwamnatin ta Nijar tace wannan wani mataki ne da ke hangen samar wa kasar cikeken ‘yancin kai a fannin cimaka a daidai lokacin da ta ke kokarin katse abin da ta kira ‘’ragowar igiyoyin mulkin mallaka’’ da a ke hasashen su na dabaibaye harakoki da dama.

Wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana Cewar, Hekta 21200 ne gwamnatin ta Nijar ta ce ta dauri aniyar bajewa domin fadada aiyukan noman zamani ba’idin hekta 10000 da tuni aka riga aka ga tasirin da suka yi wajen samar da wadatar cimaka a kasar a cewar ministan noma da kiwo kanal Mahaman Alhaji Ousman a yayin da ya ke jawabi a zauren majalissar wakilai ta rikon kwarya CCR.

Ta hanyar wannan tsari da ake saran shimfidawa a jimilce kan hekta 39700 ana hasashen girbe amfani sau biyu a kowace shekara inji ministan wanda kuma ya kara da cewa abu ne da zai bada damar samun a kalla Ton 481000 na shinkafa daga nan zuwa shekarar 2027, lamarin da ka iya rage adadin shinkafar da ke shiga kasar daga waje har ma da marasa da alkama.

Bayanan ministan sun gamsar da ‘yan majalissar kamar su Issa Adam domin a ta su fahimta zartar da kudirin gwamnatin zai samar da sassaucin rayuwa a wajen al’umma.

Galibin jama’ar Nijar sun dogara kan noma da kiwo a matsayin hanyoyin samar wa kansu cimaka sai dai matsaloli masu nasaba da canjin yanayi na haifar da babban gibin amfani, a kowace shekara idan aka kwatanta da abinda ake samu a baya abinda ke zama silar tsadar farashi a kasuwanni.

Hakan yasa shugaban kungiyar kare hakkin masaya ta ADDC Maman Nouri ke yaba wa da shirin da hukumomin suka bullo da shi.

Dam dam da manyan madatsun ruwa ne ake shirin ginawa kari akan wadanda ake da su a baya domin tabbatar da wadatar ruwan da za a yi amfani da shi a aiyukan da aka sa gaba a illahirin jihohi, kamar yadda aka yi tanadin kwararrun ma’aikata da kayan aikin noman zamani a wani bangare na aiyukan da shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya yi alkawali a kundin manufofinsa, aikin da zai lakume makuddan miliyoyin cfa.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami
Next Post: Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
  • Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.