Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar
Published: December 29, 2025 at 11:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Arewa, ya halarci wurin gwajin wasu makamai masu linzami masu cin dogon zango da kasar ta gudanar a ranar lahadi.

Kamfanin Dillancin labarai na kasar yace shugaba Kim ya bayyana cikakkiyar gamsuwarsa, a yayin da wadannan makamai masu linzami suka tashi suka bi ta inda aka auna su, kuma suka far ma inda aka yi niyya cikin teku a yamma da yankin kasar ta Koriya.

Kim ya jaddada cewa Koriya ta Arewa zata ci gaba da maida hankali kacokan wajen ingantawa da bunkasa makaman nukiliya.

Rundunar sojojin Koriya ta Kudu ta fada ranar litinin cewa dakarunta sun gano harba makamai masu linzami da aka yi da misalin karfe 8 na safiyar ranar lahadi daga yankin Sunan a kusa da Pyongyang, babban birnin Arewa.

Kamfanin dillancin labaran Yonhap na Koriya ta Kudu yace tana yiwuwa Koriya ta Arewa ta gudanar da wasu sabbin gwaje gwajen makamai masu linzami a daidai lokacin bukukuwan sabuwar shekara.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine
Next Post: An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye Labarai
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
  • Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
  • Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba Labarai
  • Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
  • Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran Afrika
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.