Ɗan Jaridar Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Najeriya Kan Rashin Ingantattun Filayen Wasanni
Wani ƙwararren ɗan jaridar Amurka, Thomas Smith, ya nuna damuwa kan halin da kayayyakin more rayuwa na ƙwallon ƙafa suke ciki a Najeriya, musamman rashin manyan filayen wasa da cibiyoyin horaswa na zamani waɗanda za su iya karɓar manyan gasannin ƙasa da ƙasa.
Smith ya ce rashin isassun kayayyakin wasanni na daga cikin abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaban ƙwallon ƙafa a Najeriya, tare da sanya ƙasar dogaro da filayen wasa na wasu ƙasashe wajen gudanar da wasannin ƙasashen duniya.
Ɗan jaridar, wanda ya ce Najeriya na da yawan jama’a da matsayi na “Gwarzon Afirka”, ya bayyana cewa ƙasar ba ta samar da isassun filayen wasa da cibiyoyin horaswa da suka dace da ƙa’idojin ƙasa da ƙasa ba.
Ya kwatanta Najeriya da ƙasashe irin su Morocco, Afirka ta Kudu da Kenya, waɗanda ya ce sun zuba jari sosai wajen inganta ababen more rayuwa na ƙwallon ƙafa, lamarin da ya sanya suke cikin ƙasashen da suka fi dacewa da karɓar manyan gasa na CAF.
Smith ya ce abin mamaki ne yadda ƙasa mai yawan jama’a kusan miliyan 243 ke fama da ƙarancin manyan filayen wasa da cibiyoyin horaswa na zamani.
Ya kuma yi tambaya kan dalilin da ya sa Najeriya, da yawan jama’arta, ba za ta iya samar da ingantattun filayen wasa da cibiyoyin horaswa ba kamar wasu ƙasashen Afirka masu ƙarancin yawan jama’a.
A cewarsa, Najeriya bai kamata ta zargi hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, CAF, da nuna mata wariya ba a lokacin da ake bai wa wasu ƙasashe damar karɓar manyan gasa saboda suna da kayayyakin more rayuwa da suka dace.
Smith ya ce kasancewar filin wasa da sauran kayan more rayuwa na zamani na daga cikin muhimman abubuwan da ake la’akari da su wajen zaɓar ƙasar da za ta karɓi manyan gasa na nahiyar.
Ya kuma bayyana dogaro da filayen wasa na ƙasashen waje wajen gudanar da wasu muhimman wasannin Najeriya a matsayin abin kunya, yana kira ga gwamnati da ta kawo ƙarshen wannan yanayi.
Ɗan jaridar ya kuma danganta matsalolin ababen more rayuwa da wasu ƙalubalen da ke fuskantar ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na ƙasa, yana cewa rashin ingantaccen tsarin bunƙasa ƙwallon ƙafa na iya rage damar gano sabbin hazaka a cikin gida.
Haka kuma, ya nuna damuwa kan yadda Najeriya ke ƙara dogaro da ’yan wasan da suka taso a ƙasashen waje, yana tambayar ko wasu daga cikinsu suna da irin ƙaunar ƙasa da alaƙar zuciya da ƙungiyar ƙasa kamar waɗanda suka taso a Najeriya.
Smith ya yi kira ga ’yan Najeriya da su riƙa neman gwamnati ta ɗauki alhakin samar da ingantattun kayayyakin ƙwallon ƙafa, yana cewa bai kamata a riƙa aro ko haya wuraren horaswa a lokacin wasannin neman gurbin shiga gasa ba.
Ya jaddada cewa filayen wasa na zamani, cibiyoyin horaswa, wuraren bunƙasa ƙwallon ƙafa na matasa da sauran kayayyakin wasanni ya kamata a ɗauke su a matsayin muhimman kadarorin ƙasa, ba wai abubuwan da ake kula da su ne kawai idan Najeriya za ta karɓi wata babbar gasa ba.
Smith ya yi gargadin cewa rashin magance matsalar ababen more rayuwa na iya yin illa ga makomar ƙwallon ƙafa a Najeriya, ciki har da rage damar ƙasar ta karɓi manyan gasannin nahiyar da kuma samun gurbin shiga manyan gasannin ƙasa da ƙasa akai-akai.
Ya yi kira da a gaggauta fara zuba jari mai ɗorewa wajen gina da gyaran filayen wasa, cibiyoyin horaswa da wuraren bunƙasa ƙwallon ƙafa tun daga matakin ƙananan yara.
A cewarsa, matsayin Najeriya a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da suka yi fice a ƙwallon ƙafa a Afirka ya kamata ya kasance tare da ingantattun kayayyakin more rayuwa da kuma ingantaccen tsarin bunƙasa ƙwallon ƙafa na dogon lokaci.


