Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka
Published: November 16, 2025 at 12:52 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Lebanon ta ce zata kai karar Isra’ila gaban Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, a saboda wata katangar da ta gina ta kankare a bakin iyakar kudancin Lebanon, wadda ta tsallake bakin iyakar da majalisar ta shata dake raba tsakanin kasashen biyu.

Wannan iyakar da ake yi ma lakabi da Shudin Layi, MDD ce ta tsara shi domin raba tsakanin Lebanon da Isra’ila, da kuma Tuddan Golan na kasar Sham wadanda Isra’ila ta mamaye. Sojojin Isra’ila sun ja, suka koma bayan wannan layin a shekarar 2000 lokacin da suka janye daga kudancin Lebanon.

Wani kakakin babban sakataren MDD, Stephane Dujarric, yace wannan katanga ta Isra’ila ta sa wasu ‘yan kasar Lebanon ba su iya shiga wasu sassan yankunansu ba.

Ofishin shugaban Lebanon ya nanata wannan a lokacin da yake ci gaba da gina wannan katanga da Isra’ila keyi ya sabawa kuduri na 1701 na Kwamitin Sulhun MDD kuma ya keta haddin diyaucin kasar Lebanon,

A ranar Jumma’a, wani kakakin rundunar sojojin bani Isra’ila, ya musanta cewa wannan katanga da ake ginawa ta tsallake wannan layi da aka shata na iyaka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza
Next Post: Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano Afrika
Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah Afrika
  • Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.