Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba!
Published: December 11, 2025 at 10:00 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 11, 2025

Ministan tsaron Somalia yace kasar ba zata amince ana wulakanta kasar ba, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya sake zagin kasar dake gabashin Afirka.

Da yake magana a wani gangami ranar talata da aka shirya a Pennsylvania, domin maida hankali kan nasarorn gwamnatinsa ta fuskar tattalin arziki, Shugaba Trump yayi Allah wadai da barin bakin haure daga kasashe matalauta su shigo Amurka.

“Muna ta karpar mutane daga Somali, wurare dake cike da fitina, ko ba hakka ba, ga dottii, da kazanta, da miyagun laifuffuka.”

Ya kara da cewa “Abunda kawai suka fi kwarewa akai shine, kama jiragen ruwa,” yana maganar kan kama jiragen ruwa a gabar tekun Somalia domiin karpar kudiin fansa.

A makon jiya ne shugaba Trump, ya bayyana ‘yan Somalia, a “zaman shara,” yace babu abunda suke yi illa bin junansu suna kashewa.”

Acikin sakon text, da ya aikawa kamfanin dillancin labarai na Reuters, ministan tsaron na Somalia Ahmed Moalli Fiqi, yace Trump ya maida hankalinsa wajen cika alkawarunda yayi wa Amurkawa mai makon bata lokacinsa kan Somalia.

Yayinda yake godewa Amurka kan taimakon da take baiwa Somalia a yaki da take yi da mayakan sakai a kasar masu alaka da kungiyar al-Qeada, yayi watsi da kalaman batanci da Trump yake yi wa kasar. Yace Somaliyawa suna fuskantar kalubale iri daban daban, amma daga karshe sna jajircewa, kuma duk inda ka same su a fadn duniya, su mutane masu aiki tukuru.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe,
Next Post: Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Malaman Tsangaya A Gombe Sun Goyi Bayan Inuwa Yahaya Da Jamilu Gwamna Afrika
AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci Labarai
‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
Gurbin Yaya Tongo: INEC Ta Tsayar Da 19 Ga Satumba Don Zaɓen Cike Gurbi Afrika
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Aikin Kwamitin Sayar Da Kaddarorin Gwamnati Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
  • Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.