Hukumar Raya Arewa maso Gabashin Najeriya (NEDC) ta ƙaddamar da shirin “Pads to Prosperity – Community Pad-Making Enterprise Programme” na matakin gwaji a Jihar Gombe, da nufin inganta lafiyar mata a lokacin haila, ƙarfafa mata da ’yan mata, tare da samar da sana’o’i masu ɗorewa a cikin al’umma.

An gudanar da shirin ne da tallafin NEDC, yayin da Virtuous Reusable Pads ke aiwatar da shi, tare da Herbloom Technologies Africa a matsayin abokin haɗin gwiwa na fasaha.
Taken shirin shi ne: “From Skills to Sustainable Enterprise – Building Health, Creating Wealth, Transforming Communities”, wato “Daga Ƙwarewa zuwa Sana’a Mai ɗorewa – Gina Lafiya, Samar da Arziki da Sauya Al’umma.”
An gudanar da bikin ƙaddamar da shirin ne tare da halartar jami’an NEDC, hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin farar hula, masu ruwa da tsaki a fannin ilimi da lafiya, da sauran wakilan al’umma.
Da yake jawabi a wajen taron, Mai Gudanar da Ayyukan NEDC a Jihar Gombe, Injiniya Usman Muhammad, ya ce shirin ya yi daidai da ƙudurin hukumar na tallafawa shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’ummar Arewa maso Gabas tare da samar da hanyoyin dogaro da kai da ci gaban tattalin arziki.
Ya ce shirin zai bai wa mata da ’yan mata ƙwarewar kera kayan tsaftar mata na zamani, tare da ilimin kasuwanci da zai ba su damar kafa sana’o’insu da samar da kuɗin shiga.
A nasa jawabin, Malam Lawal Hamidu, daga NEDC Executive, ya gabatar da jawabin buɗe taro, yayin da Dr. Constance, daga NEDC Executive, ta gabatar da babban jawabi kan muhimmancin kula da lafiyar mata a lokacin haila, samar da arziki da sauya rayuwar al’umma.
Shi ma Babban Daraktan Virtuous Reusable Pads, wanda ke wakiltar masu aiwatar da shirin, ya bayyana cewa manufar shirin ta wuce samar da kayan haila kawai, domin samar da damar kasuwanci da ƙarfafa mata ta fuskar tattalin arziki.
Haka kuma, Shugaban Shirin na Virtuous Reusable Pads ya yi bayani kan tsarin kasuwancin shirin, inda ya jaddada buƙatar sauya ƙwarewar da mahalarta suka samu zuwa sana’o’i masu ɗorewa a cikin al’umma.
A yayin taron, Mrs. Ruth Ugo, abokiyar hulɗa ta fasaha daga Herbloom Technologies Africa, ta jagoranci wani zaman gwajin inganci da nuna yadda ake kera kayan tsaftar mata bisa ƙa’idojin da suka dace.
An kuma gudanar da wani zama na musamman kan ’yan mata masu buƙatu na musamman, inda aka tattauna batun mutuncin mata a lokacin haila, samun damar amfani da kayan tsafta da kuma tabbatar da shigar da ’yan mata masu nakasa cikin shirye-shiryen irin wannan.
Haka kuma, an gudanar da zaman AGILE Strategic Spotlight, wanda ya mayar da hankali kan ilimin ’yan mata, mutuncinsu da ƙarfafa su, musamman rawar da lafiyar lokacin haila ke takawa wajen ci gaba da samun ilimi.
A nasa ɓangaren, Gombe Network of Civil Society Alhaji Ibrahim Yusuf ya jagoranci zaman musayar ƙwarewa da darussan da al’umma ta koya daga irin waɗannan shirye-shirye.
An kuma gudanar da wani zama kan sauya tallafin shiri zuwa jarin kasuwanci, wanda Alhaji Rufai Lawan Baba Manu daga NEDC ya jagoranta, inda aka jaddada muhimmancin saka jari da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki domin tabbatar da ɗorewar shirin.
ZAMAN TATTAUNAWA
A kashi na biyu na taron, Dr. Esther Ishaya ta jagoranci wani zama na tattaunawa da ya haɗa wakilai daga NOA, ilimi, lafiya, harkokin mata, AGILE da shugabannin gargajiya, inda aka tattauna hanyoyin gina ingantaccen tsarin samar da kayan tsaftar mata.
Haka kuma, Mr. Iriya Ishaya ya jagoranci wani zama da ya mayar da hankali kan sauya shirin daga aikin wucin-gadi zuwa mallakar al’umma, musamman a Gombe, Dukku, Funakaye da Yamaltu Deba.
Daga cikin muhimman abubuwan da aka gabatar akwai Strategic Showcase and Unveiling, inda jami’an NEDC da masu aiwatar da shirin suka gabatar da tsarin gine-gine da taswirar cibiyoyin sana’ar kera kayan tsaftar mata guda huɗu da za a kafa a cikin al’umma.
Mr. Lass Batti Cornelius, tare da Miss Soki Aliabo da Mrs. Ruth Ugo, sun jagoranci wani zama na haɗa kan masu ruwa da tsaki, domin samar da tsarin haɗin gwiwa mai ɗorewa.
Daga ƙarshe, wani babban jami’in NEDC ya jagoranci ƙaddamarwa da ayyana fara shirin gwaji na “Pads to Prosperity” a Jihar Gombe.
Shirin ya kuma bai wa mahalarta damar bayyana ra’ayoyinsu kan ma’anar wadata a gare su, kafin a rufe taron da godiya, yawon duba kayayyakin da aka samar, rangadin tabbatar da inganci, tattaunawa da manema labarai da kuma haɗa kan masu ruwa da tsaki.
Masu shirya shirin sun ce manufarsa ba ta tsaya ga kera kayan tsaftar mata kawai ba, sai dai gina cikakken tsari da zai haɗa ƙwarewa, tabbatar da inganci, ilimin ’yan mata, haɗa masu buƙatu na musamman, mallakar al’umma, kasuwanci, samun kasuwa da kuma kafa sana’o’i masu ɗorewa.


