Shirin Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (ACReSAL), ta hannun Jewel Environmental Initiative (JEI), ya gudanar da ayyukan kare muhalli da tallafawa harkokin kiwon lafiya a Asibitin Federal Medical Centre (FMC), Kumo, a jihar Gombe dake arewa maso Gabashin Najeriya

Ayyukan sun hada da shuka bishiyoyi, gyaran da cire laka daga magudanan ruwa, da kuma bai wa asibitin kayan amfani na kiwon lafiya, da nufin inganta tsaftar muhalli, rage tara ruwa da kuma samar da yanayi mai kyau da aminci ga marasa lafiya, ma’aikata da sauran masu ziyartar asibitin.
Da yake wakiltar Daraktan Kiwon Lafiya na FMC Kumo, Daraktan Ayyukan Jinya da Horarwa na asibitin, Dr. Nuhu Ardo Kumo, ne ya kaddamar da aikin shuka bishiyoyin, inda ya shuka bishiya ta farko. Ya samu rakiyar Shugaban Sashen Jinya, Alhaji Abdulkadir Bala Minjibir.

A yayin aikin, JEI ta kuma gudanar da aikin cire laka da tarkace daga magudanan ruwa da ke cikin harabar asibitin, lamarin da zai taimaka wajen inganta zirga-zirgar ruwa, rage hadarin tsayawar ruwa da kuma kara tsaftar muhalli.
Haka kuma, ACReSAL ta hannun JEI ta bai wa FMC Kumo kayan amfani na asibiti, ciki har da safunan tiyata (surgical gloves), domin tallafawa ayyukan kiwon lafiya da asibitin ke gudanarwa.
Da yake magana a madadin Daraktan Asibitin, Dr. Nuhu Ardo Kumo ya yabawa ACReSAL da JEI bisa wannan tallafi, yana mai cewa shuka bishiyoyi da gyaran magudanan ruwa za su taimaka wajen samar da muhalli mai tsafta, lafiya da aminci ga marasa lafiya da ma’aikatan asibitin.
Shi ma Jami’in Sa-ido da Tantance Ayyuka na JEI, Mal. Dahiru Adamu, wanda ya yi magana a madadin Babban Daraktan JEI, Alhaji Samaila Bima, ya gode wa mahukuntan FMC Kumo bisa kyakkyawar tarba da hadin kai da suka bayar wajen gudanar da aikin.
Ya kuma yaba wa jagorancin Daraktan Kiwon Lafiya na farko na asibitin, Dr. Mu’azu Shu’aibu Ishaq, bisa ci gaban da aka samu a cibiyar, tare da jaddada cewa JEI za ta ci gaba da tallafawa asibitin da ayyukan da za su inganta muhalli.
A cewarsa, irin wadannan ayyuka na cikin kokarin JEI na bayar da gudunmawa wajen cimma manufofin Majalisar Dinkin Duniya na Sustainable Development Goals (SDGs), musamman wadanda suka shafi lafiya da walwalar jama’a, tsaftataccen ruwa da muhalli, al’ummomi masu dorewa, yaki da sauyin yanayi da kare muhalli.
Aikin ya kuma nuna muhimmancin hadin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, kungiyoyin farar hula da cibiyoyin kiwon lafiya wajen kare muhalli, yaki da illolin sauyin yanayi da kuma inganta rayuwar al’umma.


