Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli
Published: January 23, 2026 at 1:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabannin kasashe dake Afirka ta tsakiya sun kammala taron koli da suka yi tare da bada umarnin a dauki matakai cikin gaggawa domin kawo daidaito ga al’amuran kudi da tattalin arziki na kasashen, domin karfafa su ganin koma baya na tattalin arzikin su, da suka hada da dawo da kudaden kasashen da suke ketare.

Shugabannin kasashen shida, sun amince da adawo da kudaden kasashen da suka samu ta fuskar albarkatun kasa, kamar yadda jawabin bayan taro na musamman da suka yi a birnin Brazaville ya nuna.

Taron kolin wadda aka gudanar karkashin laimar kungiyar raya tattalin arzikin kasashe dake Afirka ta tsakiya, an yi zaman na gaggawa domin tunkarar tafiyar hawainiyar tattalin arzikin yankin, faduwar farashin albarkatun kasa, matsalolin sakewar yanayi, da kuma tsuke bakin aljihu daga hukumomin duniya.

A bara babban bankin kasashe dake yankin Afirka ta tsakkiya, da suka hada da manyan bankunan kasashen Kamaru, da Chadi, da kasar Afirka ta tsakiya,da Gabon, da Kwango, da Equatorial Guinea, sun bukaci kamfanonin hakar mai a yankunan su adana kudaden farfado da muhalli da aka tanadar karkashi asusun babban bankin kasashen da asusun bada lamuni na duniya watau IMF a takaice, yake bada goyon baya, mataki da kamfanonin hakar man basu ji dadi ko amince dashi ba.

Kudaden wadanda kamfanonin mai din suka tanadar domin ayyukan tsabtacewa da farfado da muhalli idan aka gama hakar mai sun kai dala bilyan biyar zuwa 10.

Haka nan shugabannin sun bada umarnin hukumomin kasashen su kammala shirye shirye da yarjejeniya gamda kasafin kudi da tattalin arziki da asusun bada lamuni na duniya IMF.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC
Next Post: Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista

Karin Labarai Masu Alaka

Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.