Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli
Published: January 23, 2026 at 1:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabannin kasashe dake Afirka ta tsakiya sun kammala taron koli da suka yi tare da bada umarnin a dauki matakai cikin gaggawa domin kawo daidaito ga al’amuran kudi da tattalin arziki na kasashen, domin karfafa su ganin koma baya na tattalin arzikin su, da suka hada da dawo da kudaden kasashen da suke ketare.

Shugabannin kasashen shida, sun amince da adawo da kudaden kasashen da suka samu ta fuskar albarkatun kasa, kamar yadda jawabin bayan taro na musamman da suka yi a birnin Brazaville ya nuna.

Taron kolin wadda aka gudanar karkashin laimar kungiyar raya tattalin arzikin kasashe dake Afirka ta tsakiya, an yi zaman na gaggawa domin tunkarar tafiyar hawainiyar tattalin arzikin yankin, faduwar farashin albarkatun kasa, matsalolin sakewar yanayi, da kuma tsuke bakin aljihu daga hukumomin duniya.

A bara babban bankin kasashe dake yankin Afirka ta tsakkiya, da suka hada da manyan bankunan kasashen Kamaru, da Chadi, da kasar Afirka ta tsakiya,da Gabon, da Kwango, da Equatorial Guinea, sun bukaci kamfanonin hakar mai a yankunan su adana kudaden farfado da muhalli da aka tanadar karkashi asusun babban bankin kasashen da asusun bada lamuni na duniya watau IMF a takaice, yake bada goyon baya, mataki da kamfanonin hakar man basu ji dadi ko amince dashi ba.

Kudaden wadanda kamfanonin mai din suka tanadar domin ayyukan tsabtacewa da farfado da muhalli idan aka gama hakar mai sun kai dala bilyan biyar zuwa 10.

Haka nan shugabannin sun bada umarnin hukumomin kasashen su kammala shirye shirye da yarjejeniya gamda kasafin kudi da tattalin arziki da asusun bada lamuni na duniya IMF.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC
Next Post: Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
PDP Ta Koka Kan Rushe-rushe, Korar Gombawa Motors da Zaɓen Kananan Hukumomi A Gombe Afrika
Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
  • Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.