Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka
Published: February 13, 2026 at 5:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Afrika ta kudu Cyril Ramaphosa, ya fada jiya Alhamis cewa, zai tura sojojin kasar su taimaki ‘yan sanda wajen yaki da miyagun ayyuka a kasar, yana mai cewa wannan yana daga cikin manyan ayyuka da Gwamnatinsa da hadin guiwa zata maida hankali akai a bana.

A cikin jawabinsa ga al’ummar kasar, shugaba Ramaphosa yace tawagar farko na sojojin da za su taya ‘yansanda aiki, za’a girke su ne a lardunan yammacin Cape da kuma Guateng, inda biranen Cape Town, da Johannesburg suke.

“Kungiyoyin miyagu, sune barazana kai tsaye ga tsarin demokuradiyyar mu, ga al’umma, da kuma ci gaban tattalin arziki. Babban abunda zamu fi maida hankali akai a bana shine zafafa yaki da kungiyoyin masu aikata miyagu,” inji shugaba Ramaphosa.

Ya kara da cewa, “Na umarci ministan kula da ayyukan ‘yansanda da rundunar mayakan kasar, su bullo da tsari na inda ya kamata a yi aiki da jami’an tsaron.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Ghana Ta Tono Gold Na Miliyoyin Kudade
Next Post: Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas Labarai
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Duk Da Rauni Daya Samu Sakamakon Hari Mojtaba Khameni Yafara Aiki Labarai
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.