Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20
Published: November 21, 2025 at 4:36 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Fadar shugaban Amurka ta White House ta musanta kalamun da shugaba Cyril Ramaphosa na Afrika Ta Kudu (ATK) yayi jiya Alhamis inda yake cewa Amurka tana tunanin canja ra’ayinta game da kauracewa taron kolin kasashen kungiyar G20 a birnin Johannesburg.

A wajen wani taron manema labarai da manyan jami’an Kungiyar Tarayyar Turai jiya alhamis, shugaba Ramaphosa yace sun samu wata sanarwa daga Amurka game da canja ra’ayi ko kuma dai halartar taron a wani matsayi.

Wata jami’ar White House ta musanta wannan, tana mai cewa karamin jakadan Amurka dake Pretoria zai je wurin taron ne domin karbar ragamar jagorancin kungiyar na karba-karba wanda zai komo hannun Amurka, amma ba wai don halartar wani abu na taron ba.

Gwamnatin shugaba Trump ta ce Amurka ba zata halarci taron farko na kungiyar G20 da za a yi a Afirka ba, tana mai zargin cewa ATK mai masaukin baki, wadda turawa ‘yan tsiraru na kasar suka mulke ta har zuwa 1994, tana gallazawa da cin mutuncin turawan kasar.

Ita dai kungiyar ta G20, kungiya ce ta kasashe 19 da suka kunshi wadanda suka fi arziki da kuma wadanda tattalin arzikinsu ke tasowa sosai. A shekarar 2023, KTT da KTA, sun shiga a zaman membobi masu wakiltar kasashensu, kungiyar ta zamo mai membobi 21.

Wannan kungiya, ba kamar kungiyar G7 ta kasashe mafiya arziki zalla ba, tana mayarda hankulanta ne kan tattalin arzikin duniya da ayyukan raya kasa. Sai dai kungiyar ba ta da hedkwata, kuma ba ta cimma shawarwarin da dole membobi suyi aiki da su, abinda ya sa masu sukar lamiri suke ce kungiyar haushi kawai ta iya, ba ta da hakoran yin cizo.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025
Next Post: Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
  • “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.